ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Nijeriya Ya Fitar Da Mukalar Taya Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Nijeriya Da Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Nijeriya

Ministan harkokin wajen kasar Nijeriya Yusuf Maitama Tuggar ya fitar da mukala mai taken “Cika shekaru 55 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Nijeriya da Sin: Huldar abota ta samu ci gaba tare cikin sabon zamani”, ranar Talata a shafin jaridar China Daily, don taya murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.

A mukalarsa, ministan ya ce, tun bayan da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a tsakaninsu, sun yi ta martaba juna da cin moriyar juna, tare da bunkasa huldar kasashensu da ma inganta hadin gwiwarsu yadda ya kamata. A watan Satumban shekarar 2024, kasashen biyu sun daukaka huldarsu zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni. Lamarin da ya shaida niyyarsu ta hada hannu da juna wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakaninsu. Bunkasar huldar kasashen biyu ba bayyana burin bai daya na al’ummunsu kadai ya yi ba, har da nuna yadda kasashe masu tasowa ke dada habaka tasirinsu a duniya, wanda hakan ke da ma’ana mai muhimmanci. Ya ce, Nijeriya ta yi imanin cewa, inganta hadin gwiwarta da kasar Sin muhimmiyar dama ce ta tabbatar da dauwamammen ci gaba da ci gaban juna, kuma hakan zai samar da karin tabbas da karfi ga duniyar da ke fama da tashe-tashen hankula.

A wannan rana kuma, cibiyar nazarin harkokin kasar Sin da cibiyar nazarin harkokin zaman lafiya da daidaita rikici na Nijeriya sun shirya taron tattaunawa mai jigon “Waiwaye adon tafiya: Cika shekaru 55 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Nijeriya da Sin”, kuma mai martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da darektan sashen kula da harkokin yankin Asiya da Pasifik na ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya da ma sauran mutane sama da 100 da suka fito daga bangarori daban daban na Nijeriya sun halarci taron.

ADVERTISEMENT

Mukaddashin jakadan kasar Sin a Nijeriya, Zhou Hongyou shi ma an ba shi goron gayyata, inda ya gabatar da jawabi a wajen taron. A jawabinsa, ya ce, ran 10 ga watan Faburairu rana ce ta cika shekaru 55 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Sin da Nijeriya, kuma ministocin harkokin wajen kasashen biyu sun aika wa juna sakwannin taya murna, inda suka sake tabbatar da niyyarsu ta kara bunkasa huldar kasashen biyu cikin sabon zamani bisa daidaiton da shugabanninsu suka cimma. (Lubabatu Lei)

 

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

 

Nijeriya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
CGTN: Mafarkin Amurka Ya Lalace Zuwa Rudi Na Cin Zali

CGTN: Mafarkin Amurka Ya Lalace Zuwa Rudi Na Cin Zali

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.