A shekarar 2021, kasar Sin ta ayyana samun cikakkiyar nasara a yaki da talauci kuma ta ayyana shekaru 5 na wucin gadi a matsayin tabbatar da dorewar nasarar. Cikin wannan lokaci, gundumomi 832 masu fama da matsanancin talauci a fadin kasar sun samar tare da kafa masana’antu masu samun tagomashi, lamarin da ya kara karfafa tubalin yaki da talauci. Sakamakon wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ya nuna cewa, kaso 93.5 na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu, sun amince da nasarar Sin a yaki da talauci, a matsayin muhimmiyar gudunmuwa ga raguwar talauci a fadin duniya.
Wani bincike da bankin duniya ya gudanar ya nuna cewa zuwa shekara ta 2030, ana sa ran aiwatar da cikakkiyar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kasar Sin ta gabatar, zai fitar da mutane miliyan 7.6 na kasashen da ke cikin shawarar daga matsanancin talauci, da wasu miliyan 32 da za zu fita daga matsakaicin talauci.
A cewar nazarin na CGTN, kaso 89.1 na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu na ganin Sin a matsayin mai goyon baya da yayatawa da bayar da gudunmuwa wajen samar da al’umma mara talauci, mai makoma ta bai daya ga dan adam. Kana kaso 90.4 sun yi imanin cewa, nasarar Sin a yaki da talauci ta karfafa gwiwar duniya wajen yaki da talauci, musammam a tsakanin kasashe masu tasowa.
Mutane 9,744 ne suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24, a nazarin da kafar CGTN ta wallafa cikin harsunan Ingilishi da Sifaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci. (FMM)















Discussion about this post