ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 6: Girmama Ni’ima Da Gujewa Almubazzaranci A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon girmama ni’ima ta hanyar da ba ta saɓa da yadda muke rayuwa a sauran watanni ba. Domin lokacin da mutum yake azumi, yana jin ƙimar ruwa idan yana jin ƙishirwa, yana jin darajar abinci idan yunwa ta dame shi. Wannan yanayi yana tasar zuciya daga sakaci zuwa godiya ga Allah Ta’ãlã.

Sau da yawa mutum yana rayuwa cikin ni’imomi amma bai san ƙimarsu ba sai an ɗauke su na ɗan lokaci sai ya gane shayi ruwa ne. Ramalana na koya mana cewa ni’ima ba aba ce da za a yi wasa ko sakaci da ita ba, illa amanar da Allah da Ya ɗora mana. Yunwa da ƙishirwa da muke ɗanɗanawa a azumi suna zama makaranta ta fahimtar wahalar marasa galihu da kuma girman baiwar Allah a gare mu.

  • Darussa Daga Ramadan Na (3)
  • Darussa Daga Ramadan Na (4)

Idan lokacin buɗa-baki ya yi, muna taruruwa kan abinci cikin farin ciki. Amma wannan taruruwa ya kamata ya zama taro ne na godiya, ba taron almubazzaranci ba. Domin girmama ni’ima yana nufin:
1. Tsare ta daga ɓalɓalcewa.
2. Amfani da ita cikin tsari da adalci.
3. Godiya ga Allah a kanta da zuciya da harshe.
4. Nisantar sako-sako da wuce gona da iri.

ADVERTISEMENT

Allah Maɗaukaki Ya yi gargaɗi a cikin Alƙur’ani cewa: “Ku ci ku sha, amma kada ku yi almubazzaranci. Lalle Allah ba Ya son masu almubazzaranci.” Suratul A’rafi aya ta (31). Wannan aya tana koya mana daidaito. Musulunci ba ya hana mutum ya ji daɗin halal, amma yana hana wuce gona da iri. Ba a hana cin abinci mai daɗi ba, amma an hana ɓata shi. Ba a hana yin liyafa ba, amma an hana nuna isa da alfahari da ni’ima.

Abin takaici, a wasu lokuta na Ramalana, wanda ya zo domin koya mana jin yunwa da tausayi, sai ya koma wata na gasar girke-girke da ɓata abinci. Ana zuba abinci fiye da buƙata, ana zubar da saura ba tare da tunanin marasa galihu ba. Wannan ya sa darasin Ramalana ya ɓace a rayuwar wasu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Hakikanin girmama ni’ima shi ne ka ci ka ƙoshi, ka tuna da wanda bai samu ba. Ka rage abin da ya wuce buƙatarka, ka raba wa mabuƙata, ka kuma gode wa Allah da ya ba ka. Godiya ba kalma ba ce kawai; aiki ce. Godiya ita ce amfani da ni’ima ta hanyar da ta dace.

Ramalana wata ne na daidaito; daidaito tsakanin ibada da rayuwa, tsakanin jin daɗi da tsoron Allah, tsakanin amfani da ni’ima da kiyaye ta. Idan muka koyi wannan darasi, to bayan Ramalana ma za mu ci gaba da rayuwa cikin tsari, mu nisanci almubazzaranci, mu kuma zama masu kula da duk abin da Allah Ya hore mana.

Allah Ya sa mu zama masu girmama ni’imominSa, masu godiya a fili da a ɓoye, Ya kuma tsare mu daga wuce gona da iri. Amin.

Abu Razina Nuhu Ubale Ibrahim Paki

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Jami’in Kasar Sin: Zargin Da Kasar Amurka Ta Yi Ba Shi Da Tushe

Jami’in Kasar Sin: Zargin Da Kasar Amurka Ta Yi Ba Shi Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.