Ofishin tuntuba na babban yankin kasar Sin dake yankin musamman na Hong Kong, ya yi na’am da hukuncin da aka yankewa Jimmy Lai, bayan da wata babbar kotun HK ta same shi da laifin hada baki da sassan ketare da nufin illata tsaron kasa.
Cikin wata sanarwa, kakakin ofishin ya ce wannan ne karon farko da aka yankewa wani hukunci, bayan samunsa da laifin hadin baki da sassan ketare, karkashin dokar tsaron kasa, kuma hujjojin da aka gabatarwa kotu sun tabbatar da yadda Lai, ya hada kai da wasu sassan ketare masu adawa da kasar Sin, wajen neman a kakabawa kasar takunkumai, kana ya ci gaba da irin wadannan ayyuka bayan kaddamar da dokar.
Lai, ya kasance mai rura wutar tarzomar kin jinin Sin a Hong Kong, kuma a yau Litinin, kotu ta tabbatar masa da laifuka biyu, na makarkashiyar hadin baki da sassan ketare, da kuma kulla makircin wallafa bayanan tayar da husuma.
Da yake amsa tambayar da aka yi masa a Litinin din nan, dangane da hukuncin da kotun yankin musamman na HK ta yankewa Jimmy Lai, a gabar Birtaniya da wasu kasashen waje ke zargin rashin ’yanci a tsarin shari’a da aikin jarida a HK, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce Sin ta yi matukar Allah wadai, da bayyana adawarta, da yadda wasu kasashe ke suka da bata kimar tsarin shari’ar yankin HK. (Saminu Alhassan)













