Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa kafa rundunar ‘yan sandan jihohi zai taimaka matuƙa wajen magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya, domin hakan zai bai wa gwamnoni cikakken iko da ya dace da su matsayin su na manyan jagororin harkar tsaron jihohin su.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake matsayin ɗaya daga cikin masu tattaunawa a taron Arise News Town Hall Summit mai taken “Gina Matsaya Kan ‘Yan Sandan Jihohi da Tsaron Ƙasa”, wanda aka gudanar a ThisDay Dome da ke Abuja.
A cikin wata sanarwa da Sulaiman Bala Idris, Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfaraya fitar a ranar 9 ga Yuli, 2026, Dauda Lawal ya ce, ɗaya daga cikin manyan dalilan da suka sa rashin tsaro ya daɗe yana addabar jihohi shi ne kasancewar tsarin bayar da umarni da jagorancin jami’an tsaro ba ya ƙarƙashin gwamnoni, duk da cewa ana kiransu manyan jami’an tsaron jihohinsu.

Ya ce, idan aka bai wa gwamnatocin jihohi alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankunansu, hakan zai ƙarfafa rundunar ‘yan sanda ta fuskar kayan aiki da kuma yawan jami’an da za su iya yaƙi da miyagun laifuka.”Ana kiranmu manyan jami’an tsaron jihohi, amma tsarin bayar da umarni da jagorancin jami’an tsaro ba ya ƙarƙashin gwamnoni.
“Na yi farin ciki da ci gaban da aka samu kan batun kafa ‘yan sandan jihohi, domin hakan zai ba mu damar sauke nauyin da ke kanmu, tare da bai wa al’umma damar riƙa ɗora mana alhakin halin tsaro a jihohinmu.”
Gwamnan ya ƙara da cewa, yana da cikakken yaƙinin cewa da zarar an kafa rundunar ‘yan sandan jihohi, za ta taimaka sosai wajen shawo kan yawancin matsalolin tsaro, tare da bai wa gwamnoni damar zama manyan jami’an tsaro na haƙiƙa a jihohinsu.
Da yake mayar da martani kan fargabar cewa gwamnoni za su iya amfani da rundunar wajen musguna wa ‘yan adawa, Dauda Lawal ya ce kusan dukkan jihohin ƙasar nan na da wasu hukumomi ko rundunonin tsaro na cikin gida, amma ba a yi amfani da su wajen danne ‘yan adawa ba.

Sai dai Gwamnan ya buƙaci Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta samar da ƙa’idoji da kariya da za su hana duk wani amfani da rundunar ba bisa ƙa’ida ba.
“Ina goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi. Na fahimci damuwar da wasu ke da ita game da yiwuwar cin zarafi, amma idan aka samar da ingantattun dokoki da tsare-tsare, za a kawar da wannan fargaba.”
An shirya taron ne domin cimma matsaya kan batun kafa ‘yan sandan jihohi da kuma sauye-sauyen da suka shafi tsaron ƙasa, yayin da matsalar rashin tsaro ke ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan batutuwan da suka fi daukar hankalin ‘yan Nijeriya.
Taron ya haɗa manyan jami’an tsaro, gwamnoni, ‘yan majalisu, ƙungiyoyin fararen hula, ƙwararrun masu tsara manufofi, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna hanyoyin ƙarfafa tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin ƙasar.














