Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa Majalisar Dattawa wani ƙuduri da ke neman soke Dokar Gudanar da Shari’ar Laifuka ta 2015 (Administration of Criminal Justice Act – ACJA) tare da maye gurbinta da sabuwar Dokar Gudanar da Shari’ar Manya Laifuka ta 2026.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta wasiƙar shugaban ƙasar a zaman majalisar na ranar Alhamis, inda ya sanar da sanatoci buƙatar gwamnatin tarayya ta gaggauta duba ƙudirin.
A cikin wasiƙar, Tinubu ya bayyana cewa sabon ƙudirin na da nufin inganta tsarin gudanar da shari’ar laifuka a kotunan Babban Birnin Tarayya (FCT) da sauran kotunan tarayya a faɗin Nijeriya. Ya ce ƙudirin zai kuma kafa Majalisar da ido kan gudanar da Shari’ar . Manyan Laifuka (Administration of Criminal Justice Monitoring Council) domin tabbatar da inganci da sa ido kan yadda ake aiwatar da dokokin shari’ar manyan laifuka.
Shugaban ƙasar ya ce ƙudirin zai taimaka wajen inganta ayyukan hukumomin shari’a, da hanzarta gudanar da shari’o’in manyan laifuka, da kare al’umma daga aikata laifuffuka da kuma tabbatar da kare haƙƙin waɗanda ake zargi, da waɗanda ake tuhuma da kuma waɗanda laifi ya shafa. Haka kuma, ya ce zai ƙarfafa bin doka daga kotuna, da hukumomin tsaro da sauran cibiyoyin da ke da hannu wajen gudanar da shari’ar laifuka.
Tinubu ya bayyana cewa an yanke shawarar soke dokar ta 2015 ne bayan gano matsalolin doka, na gudanarwa da na hukumomi da suka hana aiwatar da ita yadda ya kamata. Daga cikin matsalolin akwai jinkirin bincike da gurfanar da masu laifi, ƙarancin amfani da fasaha wajen gudanar da shari’o’i, rashin ingantacciyar haɗin gwiwa tsakanin hukumomin shari’a da kuma raunin tsarin sa ido kan bin dokokin.
Bayan karanta wasiƙar, Shugaban majalisar Akpabio ya miƙa ƙudirin ga Kwamitin Majalisar Dattawa Kan Dokoki da Harkokin Majalisa, tare da umartar kwamitin da ya gabatar da rahotonsa cikin mako guda domin ci gaba da nazari kan ƙudirin.














