• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya koka game da yadda tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Jihar Filato.

Atiku, ya ce rashin daukar matakan da suka dace daga jami’an tsaro ne ke kara ruruwar wutar rikicin.

  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Ministocin Kenya
  • Ina Rokon Abba Gida-Gida Ya Dawo APC – Ganduje

LEADERSHIP HAUSA, ta ruwaito cewa rikici ya barke a Karamar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato a farkon makon nan, lamarin da ya kai ga hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da wuraren ibada.

Lamarin ya sanya gwamnan jihar, Caleb Mutfwang, ayyana dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Karamar Hukumar.

Kimanin mazauna kauyuka 30 ne aka kashe a wani kauye da ke Karamar Hukumar da sanyin safiyar Laraba duk da sanya dokar hana fita.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sai dai kuma da yake mayar da martani game da rikicin, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, ya ce ya yi takaicin tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi, inda ya bayyana hakan a matsayin cin zarafi kai-tsaye ga zaman lafiya da kuma hadin kai.

Atiku, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na X (Twitter) a ranar Alhamis, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su kara kaimi, musamman idan aka yi la’akari da yawaitar hare-haren ‘yan fashi da makami a Jihar Filato da ma sassan kasar nan.

“Na yi matukar bakin ciki da tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato duk da sanya dokar ta-baci ta sa’o’i 24.

“Wannan ta’addanci ne, wanda aka kashe rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, aka kone gidaje sannan aka jefa mutane cikin hargitsi.

“Ya zama wajibi hukumomin tsaronmu su ba da himma, musamman idan aka yi la’akari da yadda matsalar ‘yan fashin ke ci gaba da faruwa a Filato da sassan kasar nan, rashin sa ido da matakan kariya na iya kara ta’azzara lamarin.

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wadanda lamarin ya shafa, mu hada karfi da karfe domin ganin ba a sake samun irin wannan rikici ba,” in ji Atiku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuManguRikicin Filato
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Shirye Sin Take Ta Yi Aiki Da Kasashen Duniya Wajen Zurfafa Hadin Gwiwa Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

19 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.