• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya koka game da yadda tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Jihar Filato.

Atiku, ya ce rashin daukar matakan da suka dace daga jami’an tsaro ne ke kara ruruwar wutar rikicin.

  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Ministocin Kenya
  • Ina Rokon Abba Gida-Gida Ya Dawo APC – Ganduje

LEADERSHIP HAUSA, ta ruwaito cewa rikici ya barke a Karamar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato a farkon makon nan, lamarin da ya kai ga hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da wuraren ibada.

Lamarin ya sanya gwamnan jihar, Caleb Mutfwang, ayyana dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Karamar Hukumar.

Kimanin mazauna kauyuka 30 ne aka kashe a wani kauye da ke Karamar Hukumar da sanyin safiyar Laraba duk da sanya dokar hana fita.

Labarai Masu Nasaba

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Sai dai kuma da yake mayar da martani game da rikicin, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, ya ce ya yi takaicin tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi, inda ya bayyana hakan a matsayin cin zarafi kai-tsaye ga zaman lafiya da kuma hadin kai.

Atiku, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na X (Twitter) a ranar Alhamis, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su kara kaimi, musamman idan aka yi la’akari da yawaitar hare-haren ‘yan fashi da makami a Jihar Filato da ma sassan kasar nan.

“Na yi matukar bakin ciki da tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato duk da sanya dokar ta-baci ta sa’o’i 24.

“Wannan ta’addanci ne, wanda aka kashe rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, aka kone gidaje sannan aka jefa mutane cikin hargitsi.

“Ya zama wajibi hukumomin tsaronmu su ba da himma, musamman idan aka yi la’akari da yadda matsalar ‘yan fashin ke ci gaba da faruwa a Filato da sassan kasar nan, rashin sa ido da matakan kariya na iya kara ta’azzara lamarin.

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wadanda lamarin ya shafa, mu hada karfi da karfe domin ganin ba a sake samun irin wannan rikici ba,” in ji Atiku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuManguRikicin Filato
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Shirye Sin Take Ta Yi Aiki Da Kasashen Duniya Wajen Zurfafa Hadin Gwiwa Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Related

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

2 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

6 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

7 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

10 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

21 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

22 hours ago
Next Post
Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

June 27, 2025
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.