• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya koka game da yadda tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Jihar Filato.

Atiku, ya ce rashin daukar matakan da suka dace daga jami’an tsaro ne ke kara ruruwar wutar rikicin.

  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Ministocin Kenya
  • Ina Rokon Abba Gida-Gida Ya Dawo APC – Ganduje

LEADERSHIP HAUSA, ta ruwaito cewa rikici ya barke a Karamar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato a farkon makon nan, lamarin da ya kai ga hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da wuraren ibada.

Lamarin ya sanya gwamnan jihar, Caleb Mutfwang, ayyana dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Karamar Hukumar.

Kimanin mazauna kauyuka 30 ne aka kashe a wani kauye da ke Karamar Hukumar da sanyin safiyar Laraba duk da sanya dokar hana fita.

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

Sai dai kuma da yake mayar da martani game da rikicin, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, ya ce ya yi takaicin tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi, inda ya bayyana hakan a matsayin cin zarafi kai-tsaye ga zaman lafiya da kuma hadin kai.

Atiku, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na X (Twitter) a ranar Alhamis, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su kara kaimi, musamman idan aka yi la’akari da yawaitar hare-haren ‘yan fashi da makami a Jihar Filato da ma sassan kasar nan.

“Na yi matukar bakin ciki da tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato duk da sanya dokar ta-baci ta sa’o’i 24.

“Wannan ta’addanci ne, wanda aka kashe rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, aka kone gidaje sannan aka jefa mutane cikin hargitsi.

“Ya zama wajibi hukumomin tsaronmu su ba da himma, musamman idan aka yi la’akari da yadda matsalar ‘yan fashin ke ci gaba da faruwa a Filato da sassan kasar nan, rashin sa ido da matakan kariya na iya kara ta’azzara lamarin.

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wadanda lamarin ya shafa, mu hada karfi da karfe domin ganin ba a sake samun irin wannan rikici ba,” in ji Atiku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuManguRikicin Filato
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Shirye Sin Take Ta Yi Aiki Da Kasashen Duniya Wajen Zurfafa Hadin Gwiwa Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

1 hour ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

3 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

19 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

22 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

24 hours ago
Next Post
Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.