ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Filato: Atiku Ya Koka Kan Rashin Kwazon Jami’an Tsaro

by Sadiq
2 years ago
Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya koka game da yadda tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Jihar Filato.

Atiku, ya ce rashin daukar matakan da suka dace daga jami’an tsaro ne ke kara ruruwar wutar rikicin.

  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Ministocin Kenya
  • Ina Rokon Abba Gida-Gida Ya Dawo APC – Ganduje

LEADERSHIP HAUSA, ta ruwaito cewa rikici ya barke a Karamar Hukumar Mangu da ke Jihar Filato a farkon makon nan, lamarin da ya kai ga hallaka mutane da dama tare da lalata gidaje da wuraren ibada.

ADVERTISEMENT

Lamarin ya sanya gwamnan jihar, Caleb Mutfwang, ayyana dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Karamar Hukumar.

Kimanin mazauna kauyuka 30 ne aka kashe a wani kauye da ke Karamar Hukumar da sanyin safiyar Laraba duk da sanya dokar hana fita.

LABARAI MASU NASABA

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

Sai dai kuma da yake mayar da martani game da rikicin, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar adawa ta PDP, ya ce ya yi takaicin tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi, inda ya bayyana hakan a matsayin cin zarafi kai-tsaye ga zaman lafiya da kuma hadin kai.

Atiku, wanda ya bayyana hakan a shafinsa na X (Twitter) a ranar Alhamis, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su kara kaimi, musamman idan aka yi la’akari da yawaitar hare-haren ‘yan fashi da makami a Jihar Filato da ma sassan kasar nan.

“Na yi matukar bakin ciki da tashe-tashen hankula da kashe-kashen da aka yi a Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato duk da sanya dokar ta-baci ta sa’o’i 24.

“Wannan ta’addanci ne, wanda aka kashe rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, aka kone gidaje sannan aka jefa mutane cikin hargitsi.

“Ya zama wajibi hukumomin tsaronmu su ba da himma, musamman idan aka yi la’akari da yadda matsalar ‘yan fashin ke ci gaba da faruwa a Filato da sassan kasar nan, rashin sa ido da matakan kariya na iya kara ta’azzara lamarin.

“Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wadanda lamarin ya shafa, mu hada karfi da karfe domin ganin ba a sake samun irin wannan rikici ba,” in ji Atiku.

MASU ALAKA

majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Next Post
Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

Sin: Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza Shi Ne Abu Mafi Muhimmanci A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Atiku

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.