ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 75 Masu Albarka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Albarka

Gobe ke bikin cika shekaru 75 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, a wadannan shekaru 75 da suka gabata, karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), al’ummar Sinawa sun yi nasarar juyin juya halin demokradiyya, kuma sun kai matsayin da za su iya tantance makomarsu. Sai dai kuma a wannan shekarar, Dean Acheson, sakataren harkokin wajen Amurka na lokacin, a kokarin yin bayani kan musabbabin juyin juya halin kasar Sin, ta hanyar nazarin yanayin tattalin arziki da akidar kasar Sin, ya danganta juyin juya halin da abubuwa biyu wato “yawan jama’a” da “kwararar sabbin ra’ayoyi daga yamma”. Canki cankar Acheson na “yawan jama’a” ba ya da tushe. Saboda a tarihi, duk inda aka yi zalunci da cin zarafi, to dole a fuskanci turjiya, ko da yake siffofi da hanyoyin wannan turjiya na iya bambanta amma wannan ita ce mahangar tarihi.

 

Juyin juya halin dimokradiyya ta kasar Sin ya ruguje tsohon tsari da samar da wata sabuwar al’umma da za ta mallaki kasarta wadda za ta tsaya da kafafunta kuma da mutunci, kuma ita ce jigon ci gaban kasar. Kamar yadda gwamnatin kasar Sin ta sha nanata cewa, dan Adam ya fi komai daraja a duniya. Kuma karkashin jagorancin jam’iyyar JKS, muddin akwai mutane, za a iya samar da kowane irin abin al’ajabi.

ADVERTISEMENT
  • ICPC Ta Ƙulla Yarjejeniyar Haɗin Gwuiwa da Wata Hukuma A London
  • Me Ya Sa Sin Da Sauran Kasashen Duniya Ke Cin Moriya Tare a Cikin Shekaru 75 Da Suka Gabata Tun Kafuwar Sabuwar Kasar Sin?

Tun daga shekarar 1949, jam’iyyar JKS ta jagoranci al’ummar kasar wajen gaggauta farfado da tattalin arzikin kasa, wanda tsohuwar gwamnatin ta yi wa illa sosai. Duk da kasancewarta kasa mai girma da talauci mai yawan jama’a, kasar Sin ta samu ci gaba sosai wajen bin tsarin gurguzu, inda ta fara aiwatar da ayyukan gina kasar bisa tsarin gurguzu, wadanda suka shafi aikin gona na zamani, da masana’antu, da tsaron kasa, da kimiyya da fasaha.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Tun kafin kaddamar da manufar yin gyare-gyare da bude kofa ga waje a shekarar 1978, kasar Sin ta yi nasarar kafa tsarin tattalin arzikin masana’antu da na kasa mai cin gashin kansa a hankali. Kuma ta ci gaba da zurfafa gyare-gyare a fannin tattalin arziki, yayin da take ci gaba da yin gyare-gyare a harkokin mulki, da al’adu, da al’umma, da dai sauransu bisa tsarin gurguzu. A ko da yaushe ci gaban kasar Sin ya kasance yana da alaka da duniya, kamar yadda ci gaban duniya ke bukatar kasar Sin. Kasar Sin ta yi matukar tasiri a tarihin ci gaban bil Adama. Kuma ta kasance muhimmin karfi na ciyar da dan Adam gaba. (Mohammed Yahaya)

Albarka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Albarka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Amurka Ce Za Ta Yi Fama Da Mummunan Tasirin Tallafin Da Take Bayarwa Ga Neman ‘Yancin Taiwan

Amurka Ce Za Ta Yi Fama Da Mummunan Tasirin Tallafin Da Take Bayarwa Ga Neman ‘Yancin Taiwan

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.