ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Ziyarar Blinken A Kasar Sin Za Ta Bude Sabon Babin Kyautata Alakar Sin Da Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A baya bayan nan an sanar da shirin sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken na gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, ziyarar da za ta kasance mai matukar jan hankali, duba da yadda alakar Sin da Amurka ke cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu.

Yayin zantawar da ministan harkokin wajen Sin Qin Gang ya yi da Blinken a jiya Laraba, Qin ya sake jaddada matsayar kasar Sin game da yankin Taiwan, yana mai jaddada dadaddiyar aniyar kasar Sin ta kare ikon yankuna, da mulkin dukkanin sassan kasar.

  • Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken Wanda Zai Ziyarci Kasar Sin

Kafin hakan, Amurka ta sha aiwatar da matakan tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da suka hada da batun Taiwan, da yankin musamman na Hong Kong da batun jihar Xinjiang da dai sauran su.

ADVERTISEMENT

Don haka masharhanta ke ganin ziyarar aiki da Blinken zai gudanar a Sin a ranaikun Lahadi da Litinin mai zuwa, za ta ba da zarafin tattaunawa kai tsaye tsakanin bangaren Sin da na Amurka, a irin yanayi da ba kasafai ake samun sa ba.

Tabbas hakan wata dama ce ta tattaunawa, tare da warware sabani kan muhimman batutuwan dake janyo hankulan sassan biyu, musamman a wannan gaba da kasashen biyu ke fatan farfado da nagartar alakarsu.

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

A bangaren kasar Sin dai a bayyane take cewa, babu abun da kasar ke fatan cimmawa illa bunkasa dangantaka da Amurka bisa tsarin mutunta juna, da wanzar da zaman lafiya da lumana, da cimma moriyar bai daya.

Sai dai a bangaren Amurka, yanayin da ake gani daga manyan jami’an ta, da ’yan siyasar kasar na furta kalamai da fatar baki, da aiwatar da sabanin hakan, ya zamo babban dalilin dake mayar da hannun agogo baya, a kokarin da ake yi na dinke barakar kasashen biyu.

Yanzu dai abun jira a gani shi ne, ko ziyarar da Blinken zai gudanar ta wannan karo za ta share fagen warware sabani, da dora alakar sassan biyu kan turba ta gari.

Ta yadda Amurka za ta amince da dakatar da tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, da kaucewa yunkurin dakile ci gaban kasar ta hanyar sanya takunkumai marasa ma’ana, bisa fakewa da batun tsaron kasa ko wata takara maras adalci. (Saminu Hassan)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Next Post
Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.