ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Ziyarar Blinken A Kasar Sin Za Ta Bude Sabon Babin Kyautata Alakar Sin Da Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A baya bayan nan an sanar da shirin sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken na gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, ziyarar da za ta kasance mai matukar jan hankali, duba da yadda alakar Sin da Amurka ke cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu.

Yayin zantawar da ministan harkokin wajen Sin Qin Gang ya yi da Blinken a jiya Laraba, Qin ya sake jaddada matsayar kasar Sin game da yankin Taiwan, yana mai jaddada dadaddiyar aniyar kasar Sin ta kare ikon yankuna, da mulkin dukkanin sassan kasar.

  • Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken Wanda Zai Ziyarci Kasar Sin

Kafin hakan, Amurka ta sha aiwatar da matakan tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da suka hada da batun Taiwan, da yankin musamman na Hong Kong da batun jihar Xinjiang da dai sauran su.

ADVERTISEMENT

Don haka masharhanta ke ganin ziyarar aiki da Blinken zai gudanar a Sin a ranaikun Lahadi da Litinin mai zuwa, za ta ba da zarafin tattaunawa kai tsaye tsakanin bangaren Sin da na Amurka, a irin yanayi da ba kasafai ake samun sa ba.

Tabbas hakan wata dama ce ta tattaunawa, tare da warware sabani kan muhimman batutuwan dake janyo hankulan sassan biyu, musamman a wannan gaba da kasashen biyu ke fatan farfado da nagartar alakarsu.

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

A bangaren kasar Sin dai a bayyane take cewa, babu abun da kasar ke fatan cimmawa illa bunkasa dangantaka da Amurka bisa tsarin mutunta juna, da wanzar da zaman lafiya da lumana, da cimma moriyar bai daya.

Sai dai a bangaren Amurka, yanayin da ake gani daga manyan jami’an ta, da ’yan siyasar kasar na furta kalamai da fatar baki, da aiwatar da sabanin hakan, ya zamo babban dalilin dake mayar da hannun agogo baya, a kokarin da ake yi na dinke barakar kasashen biyu.

Yanzu dai abun jira a gani shi ne, ko ziyarar da Blinken zai gudanar ta wannan karo za ta share fagen warware sabani, da dora alakar sassan biyu kan turba ta gari.

Ta yadda Amurka za ta amince da dakatar da tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, da kaucewa yunkurin dakile ci gaban kasar ta hanyar sanya takunkumai marasa ma’ana, bisa fakewa da batun tsaron kasa ko wata takara maras adalci. (Saminu Hassan)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya
Daga Birnin Sin

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Next Post
Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.