ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Ziyarar Blinken A Kasar Sin Za Ta Bude Sabon Babin Kyautata Alakar Sin Da Amurka?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A baya bayan nan an sanar da shirin sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken na gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin, ziyarar da za ta kasance mai matukar jan hankali, duba da yadda alakar Sin da Amurka ke cikin wani mawuyacin hali a halin yanzu.

Yayin zantawar da ministan harkokin wajen Sin Qin Gang ya yi da Blinken a jiya Laraba, Qin ya sake jaddada matsayar kasar Sin game da yankin Taiwan, yana mai jaddada dadaddiyar aniyar kasar Sin ta kare ikon yankuna, da mulkin dukkanin sassan kasar.

  • Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken Wanda Zai Ziyarci Kasar Sin

Kafin hakan, Amurka ta sha aiwatar da matakan tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da suka hada da batun Taiwan, da yankin musamman na Hong Kong da batun jihar Xinjiang da dai sauran su.

ADVERTISEMENT

Don haka masharhanta ke ganin ziyarar aiki da Blinken zai gudanar a Sin a ranaikun Lahadi da Litinin mai zuwa, za ta ba da zarafin tattaunawa kai tsaye tsakanin bangaren Sin da na Amurka, a irin yanayi da ba kasafai ake samun sa ba.

Tabbas hakan wata dama ce ta tattaunawa, tare da warware sabani kan muhimman batutuwan dake janyo hankulan sassan biyu, musamman a wannan gaba da kasashen biyu ke fatan farfado da nagartar alakarsu.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

A bangaren kasar Sin dai a bayyane take cewa, babu abun da kasar ke fatan cimmawa illa bunkasa dangantaka da Amurka bisa tsarin mutunta juna, da wanzar da zaman lafiya da lumana, da cimma moriyar bai daya.

Sai dai a bangaren Amurka, yanayin da ake gani daga manyan jami’an ta, da ’yan siyasar kasar na furta kalamai da fatar baki, da aiwatar da sabanin hakan, ya zamo babban dalilin dake mayar da hannun agogo baya, a kokarin da ake yi na dinke barakar kasashen biyu.

Yanzu dai abun jira a gani shi ne, ko ziyarar da Blinken zai gudanar ta wannan karo za ta share fagen warware sabani, da dora alakar sassan biyu kan turba ta gari.

Ta yadda Amurka za ta amince da dakatar da tsoma baki cikin harkokin gidan kasar Sin, da kaucewa yunkurin dakile ci gaban kasar ta hanyar sanya takunkumai marasa ma’ana, bisa fakewa da batun tsaron kasa ko wata takara maras adalci. (Saminu Hassan)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Next Post
Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

Shawarwari 3 Da Shugaban Sin Ya Gabatar Kan Batun Palesdinu Sun Shaida Matsayin Sin Na Neman Adalci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.