ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

by Abubakar Sulaiman
19 hours ago

Dakarun Operation HAƊIN KAI (OPHK) tare da haɗin gwuiwar jami’an Rundunar ‘Yansandan MOPOL sun daƙile wani yunƙurin da ake zargin mayaƙan ISWAP suka yi na sace ɗalibai a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta ‘Yan Mata (FGGC), Monguno, a Jihar Borno. Jami’an tsaron sun kuma yi nasarar ceto ɗalibai 46 da aka yi yunkurin sacewa.

Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Operation HADIN KAI, Kyaftin Mohammed Goni, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na dare ranar Asabar. Ya bayyana cewa makarantar ana amfani da ita a halin yanzu a matsayin masaukin wucin gadi ga ɗaliban Federal Polytechnic Monguno, inda ya ce maharan suka kutsa cikin harabar makarantar da taimakon wasu da ake zargin masu ba su haɗin kai ne domin yin garkuwa da ɗaliban.

A cewarsa, sojoji da jami’an MOPOL sun yi gaggawar tunkarar maharan, sannan dakarun Quick Reaction Force na Sector 3 suka isa domin ƙarfafa gudummawar. Hakan ya tilasta wa maharan tserewa ba tare da sun cimma manufarsu ba. An kwashe dukkan ɗaliban zuwa Barikin Kinnasara da ke Monguno, inda aka duba lafiyarsu tare da ba su kulawar da ta dace.

ADVERTISEMENT

Sai dai Kyaftin Goni ya bayyana cewa duk da cewa ba a yi garkuwa da wani ɗalibi ba, wasu daga cikin ɗaliban sun rasa rayukansu sakamakon harbin da maharan suka riƙa yi kan mai uwa da wabi yayin musayar wuta. Ya ƙara da cewa wasu sassan gine-ginen makarantar sun lalace.

Ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar maharan da kuma binciken waɗanda ake zargin sun ba su haɗin kai, tare da jaddada cewa Operation HAƊIN KAI zai ci gaba da matsa wa ƙungiyoyin ta’addanci lamba a yankin Arewa maso Gabas.

LABARAI MASU NASABA

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
  • Abubakar Sulaiman
    ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya
  • Abubakar Sulaiman
    NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

MASU ALAKA

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
Manyan Labarai

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya
Labarai

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

July 20, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Next Post
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026
ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

July 20, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.