Dakarun Operation HAƊIN KAI (OPHK) tare da haɗin gwuiwar jami’an Rundunar ‘Yansandan MOPOL sun daƙile wani yunƙurin da ake zargin mayaƙan ISWAP suka yi na sace ɗalibai a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta ‘Yan Mata (FGGC), Monguno, a Jihar Borno. Jami’an tsaron sun kuma yi nasarar ceto ɗalibai 46 da aka yi yunkurin sacewa.
Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Operation HADIN KAI, Kyaftin Mohammed Goni, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na dare ranar Asabar. Ya bayyana cewa makarantar ana amfani da ita a halin yanzu a matsayin masaukin wucin gadi ga ɗaliban Federal Polytechnic Monguno, inda ya ce maharan suka kutsa cikin harabar makarantar da taimakon wasu da ake zargin masu ba su haɗin kai ne domin yin garkuwa da ɗaliban.
A cewarsa, sojoji da jami’an MOPOL sun yi gaggawar tunkarar maharan, sannan dakarun Quick Reaction Force na Sector 3 suka isa domin ƙarfafa gudummawar. Hakan ya tilasta wa maharan tserewa ba tare da sun cimma manufarsu ba. An kwashe dukkan ɗaliban zuwa Barikin Kinnasara da ke Monguno, inda aka duba lafiyarsu tare da ba su kulawar da ta dace.
Sai dai Kyaftin Goni ya bayyana cewa duk da cewa ba a yi garkuwa da wani ɗalibi ba, wasu daga cikin ɗaliban sun rasa rayukansu sakamakon harbin da maharan suka riƙa yi kan mai uwa da wabi yayin musayar wuta. Ya ƙara da cewa wasu sassan gine-ginen makarantar sun lalace.
Ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar maharan da kuma binciken waɗanda ake zargin sun ba su haɗin kai, tare da jaddada cewa Operation HAƊIN KAI zai ci gaba da matsa wa ƙungiyoyin ta’addanci lamba a yankin Arewa maso Gabas.














