Wani matashi mai shekara 13 ya rasu, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon rugujewar wani abun hawa a lokacin murnar nasarar da tawagar ƙwallon ƙafa ta Spain ta samu a Gasar Kofin Duniya.
Lamarin ya faru ne a wani gari da ke yammacin ƙasar Spain, kamar yadda hukumomin yankin da kafafen yaɗa labarai suka bayyana a ranar Litinin.
Majalisar Birnin Ciudad Rodrigo ta bayyana alhini kan rasuwar yaron cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook, inda ta miƙa ta’aziyya ga iyalansa.
Sanarwar ta ce, “Abin da ya kamata ya zama ranar farin ciki saboda nasarar tawagar Spain a Gasar Kofin Duniya ya rikide zuwa babban abin takaici.” Ta kuma tabbatar da cewa wasu mutane da dama sun samu raunuka a lamarin.
Rahotannin kafafen yaɗa labarai na yankin sun ce abun hawan ya rushe ne bayan mutane masu yawa sun hau samansa domin murnar nasarar da Spain ta samu, wadda ita ce nasararta ta farko a Gasar Kofin Duniya tun bayan shekarar 2010.














