ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

by Khalid Idris Doya
19 hours ago

Gwamnatin Jihar Bauchi ta musanta jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta da cewa ta na shirin mayar da reshen Jami’ar Sa’adu Zungur (SAZU) da ke Yuli a cikin garin Bauchi zuwa harabar dindindin ta jami’ar da ke Gadau.

Haka kuma, gwamnatin ta ƙaryata bayanan da suke yaɗuwa da ke cewa ta sayar ko za a sayar da reshen Jami’ar na Yuli ga fitaccen attajiri, Alhaji Aliko Dangote, tana mai bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya tsagwaronta, kuma mara tushe balle makama.

Kwamishiniyar ma’aikatar kula da manyan makarantun gaba da sakandare, Dakta Hadiza Abdulkadir Kango, ta musanta wannan zargi a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi.Sanarwar da Jami’in yaɗa labarai na ma’aikatar, Awwal Sani Waziri, ya sanya wa hannu ta ja hankalin jama’a da su yi watsi da jita-jitar da ake cewa za tashi reshen Bauchi (Yuli) ta Jami’ar Sa’adu Zungur zuwa Gadau kuma a sayar da reshen makarantar.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatar ta bayyana cewa wasu masu son tayar da fitina daga ciki da wajen jami’ar ne suka ƙirƙiri wannan labari domin haifar da rashin jituwa da kuma cimma muradunsu na ƙashin kansu ta hanyar yaɗa labaran ƙarya.Kwamishiyar ta ma’aikatar kula da ilimi mai zurfi ta kuma yi Allah-wadai da wannan batun tare da kira ga al’umma da su yi watsi da jita-jitar, tana mai jaddada cewa an ƙirƙire ta ne da gangan domin yaudarar jama’a.

Dakta Kango ta bayyana cewa hukumomin da abin ya shafa sun fara bincike domin gano waɗanda suka ƙirƙiri da kuma yaɗa wannan bayanin na ƙarya, inda za a ɗauki matakin doka a kansu idan ya zama dole.

LABARAI MASU NASABA

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

Ta kuma tabbatar da cewa gwamnatin Jihar Bauchi ba ta da wani shiri na mayar da ko sayar da reshen Jami’ar ta Yuli.A maimakon haka, ta ce gwamnati na ci gaba da jajircewa wajen bunƙasa reshen Jami’ar, inda ta tsara gudanar da ayyukan gina hanyoyin shiga harabar, ɗakin kwanan ɗalibai mata da kuma katanga domin inganta walwalar ɗalibai, yanayin koyo da kuma tsaro.

Kwamishiniyar ta kuma gode wa jama’ar da suka gaggauta sanar da ma’aikatar game da wannan jita-jita, tare da yin kira ga mazauna jihar su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen ƙarfafa ilimi mai zurfi a Jihar Bauchi.

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya
Manyan Labarai

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

LABARAI MASU NASABA

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.