Gwamnatin Jihar Bauchi ta musanta jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta da cewa ta na shirin mayar da reshen Jami’ar Sa’adu Zungur (SAZU) da ke Yuli a cikin garin Bauchi zuwa harabar dindindin ta jami’ar da ke Gadau.
Haka kuma, gwamnatin ta ƙaryata bayanan da suke yaɗuwa da ke cewa ta sayar ko za a sayar da reshen Jami’ar na Yuli ga fitaccen attajiri, Alhaji Aliko Dangote, tana mai bayyana iƙirarin a matsayin ƙarya tsagwaronta, kuma mara tushe balle makama.
Kwamishiniyar ma’aikatar kula da manyan makarantun gaba da sakandare, Dakta Hadiza Abdulkadir Kango, ta musanta wannan zargi a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi.Sanarwar da Jami’in yaɗa labarai na ma’aikatar, Awwal Sani Waziri, ya sanya wa hannu ta ja hankalin jama’a da su yi watsi da jita-jitar da ake cewa za tashi reshen Bauchi (Yuli) ta Jami’ar Sa’adu Zungur zuwa Gadau kuma a sayar da reshen makarantar.
Ma’aikatar ta bayyana cewa wasu masu son tayar da fitina daga ciki da wajen jami’ar ne suka ƙirƙiri wannan labari domin haifar da rashin jituwa da kuma cimma muradunsu na ƙashin kansu ta hanyar yaɗa labaran ƙarya.Kwamishiyar ta ma’aikatar kula da ilimi mai zurfi ta kuma yi Allah-wadai da wannan batun tare da kira ga al’umma da su yi watsi da jita-jitar, tana mai jaddada cewa an ƙirƙire ta ne da gangan domin yaudarar jama’a.
Dakta Kango ta bayyana cewa hukumomin da abin ya shafa sun fara bincike domin gano waɗanda suka ƙirƙiri da kuma yaɗa wannan bayanin na ƙarya, inda za a ɗauki matakin doka a kansu idan ya zama dole.
Ta kuma tabbatar da cewa gwamnatin Jihar Bauchi ba ta da wani shiri na mayar da ko sayar da reshen Jami’ar ta Yuli.A maimakon haka, ta ce gwamnati na ci gaba da jajircewa wajen bunƙasa reshen Jami’ar, inda ta tsara gudanar da ayyukan gina hanyoyin shiga harabar, ɗakin kwanan ɗalibai mata da kuma katanga domin inganta walwalar ɗalibai, yanayin koyo da kuma tsaro.
Kwamishiniyar ta kuma gode wa jama’ar da suka gaggauta sanar da ma’aikatar game da wannan jita-jita, tare da yin kira ga mazauna jihar su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen ƙarfafa ilimi mai zurfi a Jihar Bauchi.














