Dakarun Operation Hadin Kai sun kama wani ɗan ƙasar Sudan mai shekaru 32, Musa Fashir, da wata ’yar ƙasar Ghana mai shekaru 36, Mary Florence, yayin wani samame na tsaro da suka gudanar a Ƙaramar Hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno.
Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana cewa ana zargin Musa Fashir da kasancewa mayaƙin ta’addanci daga ƙasar waje tare da haɗa kai da ’yan ta’adda, yayin da ake zargin Mary Florence da zama a Nijeriya ba bisa ƙa’ida ba.
Mukaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Operation Hadin Kai, Kyaftin Muhammed Goni, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.
A cewarsa, dakarun Bataliya ta 115 ta rundunar sun kama mutanen biyu da misalin ƙarfe 11:48 na safe a ranar Asabar, 19 ga Yuli, a garin Lassa da ke yankin Dille na Ƙaramar Hukumar Askira/Uba.
Ya ce samamen wani ɓangare ne na ci gaba da gudanar da ayyukan yaƙi da ta’addanci bisa bayanan sirri, da nufin tarwatsa ayyukan ’yan tada ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.














