Tawaga ta 17 ta jami’an lafiya ta Sin a Burkina Faso, ta bayar da gudunmuwar kayayyakin lafiya ga asibitin koyarwa na jami’ar Tengandogo, domin inganta ayyukan kiwon lafiya.
Jakadan Sin a Burkina Faso Zhao Deyong da ministan lafiya da kula da tsaftar al’umma na kasar Robert Lucien Jean-Claude Kargougou, sun halarci bikin bayar da gudunmuwar wanda aka yi ranar Juma’a a Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso.Yayin bikin, tawagar ta bayar da gudunmuwar kayayyakin lafiya da darajarsu ta kai CFA francs miliyan 32, kwatankwacin dalar Amurka 56,000, wadanda suka hada da kayayyakin ganowa da jinyar cuttukan zuciya da sauran kayayyakin kula da marasa lafiya.
Da yake jawabi, ministan lafiya na Burkina Faso ya yabawa nasarorin da aka samu daga hadin gwiwar kasashen biyu a bangaren lafiya, ya kuma bayyana sahihiyar godiya ga taimakon da Sin ke ba kasar wajen samar da kayayyakin asibiti da musayar ilimi da horar da jami’ai da samar da magunguna, yana mai fatan ganin karin kyawawan hadin gwiwa a tsakaninsu a bangaren kiwon lafiya. (Fa’iza Mustapha)














