Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun, ya bayyana a wani taron manema labarai na yau da kullum da ya gudana yau Jumma’a cewa, Sin ta bukaci Japan ta fuskanci tarihinta na mamayar zalunci tare da yin waiwaye mai zurfi a kai, sannan ta yi kokarin samun yardar makwabtanta na Asiya da kuma kasashen duniya baki daya ta hanyar daukar kwararan matakai na zahiri.
Guo ya bayyana cewa, musanta laifin mamayar zalunci na nufin kalubalantar abubuwan da aka kammala tabbatarwa a tarihi da kuma kawo cikas ga tsarin kasa da kasa da aka kafa bayan yakin duniya na biyu, inda ya jaddada cewa, dole ne dukkan kasashen yankin, ciki har da kasar Sin, su kasance cikin matukar taka-tsantsan, tare da hana sake ganin tara karfin soji na Japan da kuma hana sake barin masifun da suka faru a tarihi su maimaita kansu.
A yau Jumma’a, an kunna jiniya da kada kararrawa a yankin arewa maso gabashin kasar Sin domin cika shekaru 95 da faruwar al’amarin ranar 18 ga watan Satumba, wanda ya zama farkon yakin turjiyar kasar Sin ga mamayar zaluncin kasar Japan.
A ranar 18 ga watan Satumbar 1931 ne dai sojojin Japan suka tarwatsa wani bangare na layin dogo da ke karkashin ikonsu a kusa da birnin Shenyang, inda suka zargi sojojin kasar Sin da yin zagon kasa don kawai su samu hujjar harin da suka kai sansanin soji da ke kusa da Shenyang a ranar da dare, tare da kaddamar da mamayar da suka shirya munakisarta tun farko a kan kasar Sin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)













