A yau Jumma’a ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda game da halin da ake ciki a duniya, ya ce duk da sauye-sauyen hali da ake ciki, kasar Sin za ta dade tana samar da tabbaci ga duniya mai cike da sauye-sauye, tare da bayar da damammaki, da kwarin gwiwa, da kuma karfi ga ci gaban kasashen duniya tare bisa bunkasar kanta.
Game da kalaman shugaban Amurka Donald Trump na cewa Amurka na shirin tura sojoji zuwa Iran, Guo ya ce bangaren Sin na fatan Iran za ta wanzar da kwanciyar hankalin yankunanta, su kuma bangarorin duniya daban daban za su kiyaye zaman lafiya, su yi taka-tsantsan, da warware rikici ta hanyar tattaunawa.
Bugu da kari, game da kalaman da wasu kwararrun MDD suka yi, cewa wai “An tilasta wa mutane yin aikin dole”, Guo ya ce, gwamnatin Sin ta dade tana himmatuwa wajen inganta da kiyaye hakkin bil’adama. Kuma “Damuwa” ta wasu kwararru karya ce kawai marar tushe ko kadan. (Safiyah Ma)















Discussion about this post