Dakarun Sojin Operation Fansan Yamma sun ceto wasu manoma bakwai da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a ƙauyen Gandi, da ke ƙaramar hukumar Rabah a Jihar Sakkwato.
Majiyoyin tsaro sun ce sojojin rundunar 8 ne suka gaggauta kai ɗauki bayan harin, inda suka fafata da ’yan bindigar.
A yayin farmakin, sojojin sun ƙwato wasu babura da ake zargin ’yan bindigar sun yi amfani da su wajen kai harin.
An ceto dukkanin manoman bakwai lafiya.
Sai dai an samu wani farar hula da ya samu raunin harbin bindiga a lokacin artabun.
An garzaya da shi asibitin gwamnati na Gandi, inda yake karɓar magani.
Hukumomi sun ce wannan farmaki na daga cikin ƙoƙarin da ake yi wajen yaƙi da ’yan bindiga da tabbatar da tsaro a Arewa maso Yamma.
Haka kuma sun shawarci mazauna yankin da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanan da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankunan da ke fuskantar matsalar tsaro.













Discussion about this post