Dakarun rundunar ‘Operation Fansan Yamma’ sun ceto manoma bakwai da aka yi garkuwa da su yayin wani hari da ’yan bindiga suka kai kan al’ummar Gandi da ke ƙaramar hukumar Rabah a Jihar Sokoto.
Wata majiya ta tsaro ta bayyana cewa sojojin Runduna ta 8 ta Sojojin Nijeriya da ke sansanin Gandi ne suka gudanar da nasarar aikin ceton bayan sun samu rahoton harin.
A cewar majiyar, dakarun sun yi artabu da ’yan bindigar tare da kwato wasu babura da dama da ake zargin maharan suna amfani da su wajen kai harin.
Aikin ceton ya kai ga kuɓutar da dukkan manoman bakwai cikin ƙoshin lafiya, lamarin da ya hana su shiga dogon zaman garkuwa da mutane a hannun ‘yan ta’addan.













Discussion about this post