Gwamnatin Tarayya ta musanta rahotannin da ke cewa tana shirin ƙaƙaba sabbin haraji kan man fetur da kuma kiran waya da data.
Bayanin ya biyo bayan wasu rahotanni da suka ce Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya ba da shawarar a sanya Harajin VAT ka man fetur da kuma harkokin sadarwa domin ƙara kuɗaɗen shiga na gwamnati.
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Kuɗi ta fitar a ranar Laraba, gwamnatin ta ce rahotannin sun ba da bayanan da ba su dace ba kuma ba su nuna manufar gwamnati ba.
Ma’aikatar ta bayyana cewa IMF ya gabatar da shawarwari ne kawai a cikin rahotonsa kan tattalin arziƙin Nijeriya, kuma irin waɗannan shawarwari ba wajibi ba ne gwamnatin ta aiwatar da su.
Gwamnatin ta jaddada cewa har yanzu rangwamen VAT kan man fetur yana nan daram kuma ba a soke shi ba.
Haka kuma, ta ce babu wani shiri a halin yanzu na ƙaƙaba ƙarin haraji kan man fetur.
Bugu da ƙari, ma’aikatar ta ce haraji na musamman kan harkokin sadarwa da aka gabatar kafin shekarar 2023 an riga an soke shi a ƙarƙashin sabbin dokokin haraji.
Saboda haka, gwamnatin ta buƙaci ‘yan Nijeriya su yi watsi da rahotannin da ke cewa ana shirin ƙaƙaba sabbin haraji kan man fetur ko harkokin sadarwa.
Ta ƙara da cewa abin da ta sa a gaba shi ne bunƙasa tattalin arziƙi, inganta tattara kuɗaɗen shiga, rage asarar kuɗaɗe da samar da ayyukan yi, maimakon ƙara wa jama’a haraji.
Sanarwar ta tabbatar da cewa duk wani sabon matakin haraji da za a ɗauka a nan gaba za a sanar da shi ne a hukumance kuma bisa tanadin doka.













Discussion about this post