Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun ceto wasu mutane da aka yi garkuwa da su, sun dakile wani yunkurin satar mutane, tare da kama wasu da ake zargi da samar wa ‘yan ta’adda kayan aiki yayin da suke jigilar babura guda 10 a wasu hare-haren tsaro da aka gudanar a jihohin Zamfara, Katsina da Kebbi.
Rundunar Hadin Gwiwa ta Yankin Arewa maso Yamma (Joint Task Force North West) ta bayyana nasarorin cikin wata sanarwa da Jami’in Yada Labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar a ranar Talata.
Sanarwar ta ce an gudanar da wadannan ayyukan ne tsakanin ranakun 19 da 20 ga watan Yuli, a matsayin wani ɓangare na ci gaba da kokarin katse hanyoyin ayyukan ‘yan ta’adda da kuma hana kungiyoyin masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Yammacin Nijeriya.














