Rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi ta kama wani mutum mai suna Clement Anthony, mai shekaru 40 a duniya, bisa zarginsa da hannu a kisan wani mutum mai shekaru 55 da kuma mallakar bindiga ƙirar gida ba bisa ƙa’ida ba a cikin garin Bauchi.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SP Nafiu Habib, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata. Ya ce wani mazaunin unguwar Ngas da ke cikin ƙaramar hukumar Bauchi ne ya kai labarin faruwar lamarin ga ofishin ‘uansanda ta ‘A’ Division a ranar 19 ga Yuli, 2026.
Sanarwar ta ce mai shigar da ƙorafin ya shaida wa ‘yansanda cewa akwai zargin cewa Clement Anthony, mazaunin Unguwar Ngas, Inkil, Bauchi, ya ɗauki wata bindiga ƙirar gida mai harsashi guda (harbi-ka-noƙe), sannan da gangan ya ɗambara alburushin wa Malam Jacob Bature, mai shekaru 55, wanda shi ne mai unguwar Ngas, yayin wata taƙaddama da ta shiga tsakaninsu.
Jacob ya samu munanan raunukan harbin bindiga a gefen dama na ƙirjinsa, inda ya faɗi a sume. Daga nan aka garzaya da shi zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.
SP Nafiu Habib ya ƙara da cewa an ajiye gawar mamacin a ɗakin ajiyar gawa na asibitin domin ci gaba da bincike.
Jami’an ‘yansanda sun yi gaggawar kama wanda ake zargin, tare da ƙwato bindigar ƙirar gida mai harsada ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata laifin, da kuma kwanson harsashi guda da aka harba.
Nafiu ya ce an miƙa kes ɗin zuwa sashen binciken manyan laifuka (SCID) domin ci gaba da zurfafa bincike. Ya ce za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yi Allah wadai da kisan, tare da jaddada ƙudirin rundunar na tabbatar da cewa duk masu aikata laifuka suna fuskanci hukunci bisa doka.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su guji mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba, tare da gaggauta kai rahoton duk wani mutum ko abu da ake zargi da shi zuwa ofishin ‘yansanda mafi kusa.














