Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutun aiki a jihar domin girmama marigayi Alhaji Bamanga Tukur.
Tukur, wanda ya kasance dattijo, tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa, kuma tsohon gwamnan Gongola, an yi jana’izarsa tare da binne shi a Yola ranar Lahadi bayan gudanar da sallar jana’iza a Masallacin Fadar Lamidon Adamawa.
A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Humwashi Wonosikou, ya fitar, Fintiri ya ce an ayyana hutun ne domin bai wa al’ummar jihar damar yin zaman makoki tare da tunawa da rayuwarsa da irin gudunmawar da ya bayar.
Gwamnan ya bayyana Tukur a matsayin ɗan ƙasa mai kishin jiha da ƙasa, yana mai cewa gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Adamawa da Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa.
Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su yi amfani da ranar hutun wajen yi wa marigayin addu’ar Allah Ya gafarta masa, Ya kuma ba iyalansa, abokansa da al’ummar Adamawa haƙurin rashinsa.














