ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

by Abubakar Sulaiman
6 hours ago
MACBAN

Ƙungiyar Miyetti Allah (MACBAN), reshen Jihar Kaduna, ta ce makiyaya sun rasa sama da shanu 200,000 tsakanin Janairu zuwa Satumban 2026 sakamakon satar shanu, da hare-haren ’yan bindiga, da rikicin manoma da makiyaya da sauran matsalolin tsaro.

Shugaban MACBAN na Jihar Kaduna, Alhaji Abdulhamid Musa Albarka, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna. Ya kuma ce an kashe akalla mambobin ƙungiyar 50 a cikin wannan lokaci, inda ya danganta da rikice-rikicen al’umma, da hare-haren manoma da kuma kisan da ’yan bindiga ke yi yayin satar shanu.

Ƙungiyar ta ce asarar shanun ta jefa iyalai da dama cikin matsanancin talauci, ganin cewa kiwon dabbobi shi ne babbar hanyar samun abin dogaro ga yawancin makiyayan da abin ya shafa. Ta bayyana Kachia, da Chikun, da Kagarko, da Giwa, da Igabi, da Jama’a, da Kaura, da Sanga, da Jaba, da Kudan, da Makarfi, da Lere, da Zangon Kataf da Kauru a matsayin wasu daga cikin wuraren da matsalar ta fi shafa.

ADVERTISEMENT

MACBAN ta kuma nuna damuwa kan kasuwar dabbobi ta Rijana da ke Ƙaramar Hukumar Kachia, tana mai kira ga gwamnati da jami’an tsaro su tabbatar da cewa ba a amfani da kasuwar wajen sayar da dabbobin da aka sace. Sai dai ta jaddada cewa ba ta zargi dukkan ’yan kasuwa ko masu dabbobi da ke kasuwar da hannu a aikata laifi ba.

Ƙungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da hukumomin tsaro da su ƙara ayyukan leƙen asiri da samame a wuraren da ake yawan satar shanu, tare da samar da hanyoyin gano da dawo da dabbobin da aka sace ga masu su. Ta kuma buƙaci a kafa kwamiti da zai tantance yawan dabbobin da aka rasa da iyalan da matsalar ta shafa.

LABARAI MASU NASABA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

MACBAN
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan
  • Abubakar Sulaiman
    Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

MASU ALAKA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
MACBAN
Labarai

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya
Labarai

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Next Post
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki - Gwamna Alia Ga Ortom

LABARAI MASU NASABA

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
MACBAN

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
MACBAN

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
MACBAN

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.