Bikin baje kolin kasa da kasa kan kasuwancin ba da hidimomi na kasar Sin na shekarar 2026 (CIFTIS), wanda ya gudana a Beijing, babban birnin kasar Sin, daga ranar 9 zuwa 13 ga watan Satumba, ya zurfafa cimma matsaya kan karfafa hadin gwiwa a fannin ba da hidimomi tare da sanya kuzari ga tattalin arzikin duniya.
An samu sakamako mai kyau a yayin wannan baje koli na tsawon kwana biyar, wanda ya kunshi gudanar da tarurruka da tattaunawar dandaloli kusan 100, tare da gudanar tarurruka na harkokin haduwa da abokan kasuwanci da tallata hajoji, kamar yadda Zhu Guangyao, jami’i a ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin, ya bayyana a wani taron manema labarai da aka gabatar bayan kammala baje kolin.
Zhu ya bayyana cewa, taron wanda ya samu nasara ya aike da sako baro-baro a fili ga duniya cewa, kasar Sin za ta ci gaba da fadada manufar bude kofa mai matukar inganci ba tare da ja da baya ba, da kuma karfafa samun ci gaba mai matukar inganci.
A cewar shugaban kasar Burundi, Evariste Ndayishimiye, wanda har ila yau shi ne shugaban kungiyar Tarayyar Afirka (AU) na yanzu, CIFTIS, a matsayin daya daga cikin manyan dandalolin duniya na cinikayyar ba da hidimomi, ya kunshi hangen nesa na bude kofa, da hadin gwiwa, da ci gaba na bai-daya.
Ya kuma bayyana cewa, ta hanyar hada gwamnatoci, da hukumomin kasa da kasa, da masu zuba jari wuri guda, wannan baje koli yana samar da wata dama ta musamman ta musaya da raba kwarewa ga juna, tare da samar da sabbin damammaki. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














