Rundunar ‘Yansandan Jihar Zamfara ta ƙaddamar da aikin ceto limamai shida da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi garkuwa da su a ƙaramar hukumar Bakura ta jihar.
An yi garkuwa da limaman ne da misalin ƙarfe 11:30 na safe ranar Asabar, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Talata Mafara ta hanyar Dakko–Damri da ke ƙaramar hukumar Bakura.
A cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar ‘Yansandan jihar, Yazid Abubakar, ya fitar ranar Asabar a Gusau, ya ce jami’an tsaro tare da jami’an sa-kai da ‘Community Rescue Unit’ da sauran hukumomin tsaro sun fara wani aikin ceto na musamman domin gano inda aka kai limaman da kuma tabbatar da an kubutar da su.
Ya ce maharan sun yi kwanton bauna ne a kan hanyar Dakko–Damri, inda suka tare motar da limaman ke ciki tare da yin garkuwa da su.
Rundunar ta ce tana ci gaba da bincike da sintiri a yankin domin ganin an kubutar da limaman cikin ƙoshin lafiya.
In ba a manta ba dai, a jiya Lahadi mun rahoto cewa, an yi garkuwa da malaman ne akan hanyarsu ta komawa gida bayan sun kammala taro da Daraktan Kamfen din shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ke neman tazarce a karkashin inuwar jam’iyyar APC.
ADVERTISEMENT














