ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimako Ko Barna?

by Sulaiman Bala Idris
4 years ago
Barna

Idan ka gabatar da wannan maudu’in a matsayin tattaunawa a Nijeriya, musamman a Arewacin Nijeriya zai zama wani bakon abu ne har ma ya zama tasirinshi zai iya razana kwakwale ko kuma ya jefa mutum cikin dogon tunani mai sarkakiya, cakude da shakku a kan anya hakan na aukuwa kuwa?

Ba mutum gudummawa ya halaka kanshi ‘Assisted Suicide’ ya na nufin hadin gwiwa tsakanin wanda ke son ya kashe kanshi da wani mutum domin hakar wanda ke son mutuwan ta cimma ruwa.

  • Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?
  • Masarautar Mubi Da Kyakkyawan Shugabancin Sarki Alhaji Abubakar Isa Ahmadu

Abin da a ke nufi da halaka kai bisa zabin rai ‘suicide’ shi ne mutum ya yi sanadin mutuwar kanshi da kanshi.

ADVERTISEMENT

Akwai bambanci tsakanin mutum ya halaka kanshi bisa zabi ‘suicide’ da kuma kisan da sai an bashi gudummawa wurin halaka kanshi din ‘Assisted suicide’.

Neman tallafin wani domin mutum ya halaka kanshi ya na aukuwa ne a mafi yawancin lokuta yayin da wata cuta wacce ta ki ci ta ki cinyewa ta addabe shi.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Idan har mutum ya na sane ya ba wani gudummawa ko da da shawara ce, wacce ta yi sanadiyyan halakarshi a doka su biyun ne ke da alhakin kisan.

An fi samun irin wannan a asibiti, inda likitoci kan ba marasa lafiya magunguna ko allurar da za ta katse masu rayuwa.

Duk da ba a asibiti kadai a ke aikata irin wannan ba, amma a can din a ka fi yin haka.

Marasa lafiya da ke fama da miyagun cututtuka, su kan cire tsammanin cewa likitoci za su iya taka wata muhimmiyar rawa ga samuwar lafiyarsu, da irin wannan tunanin ne su ke hana likitoci su gabatar da aikin da ya dace akansu.

A na iya ganin haka yawanci ga masu cututtukan kansa, da nakasan wani muhimmin bangare na jikin dan Adam.

Da yawan marasa lafiyan da kan nemi gudummawar likitoci don a katse rayuwarsu su na yin haka ne saboda matsanancin radadin cutar da ke addabarsu, ba tare da yin la’akari da rashin tabbas na abin da za su je can su taras ba.

A wani bangare na nazarin kuma, akwai wadanda ke kashe mai jinya bisa dalilin wai su na tausayin wannan mara lafiyan a kan wahalhalu da azaban ciwo da ya ke fama da su.

Likitoci na yin irin wannan a wasu lokutan ta hanyar yin allura.

A na kiran irin wannan kisa da ‘Euthanasia’.

Mafi yawa irin wannan, dangin mara lafiyan ne su ke gabatarwa da likitocin da bukatar a katse a rayuwar majinyacinsu, saboda ya na wahalar da su, kuma ciwon babu alamar samun sauki.

Hatta a tsakankanin masana tun a }arnonin baya akwai taraddadi da shakka kan ra’ayin kisa don tausayi, don wahalar rayuwa ko kuma don radadin ciwo.

Ko kadan a lokutan baya ba a yi sakacin aminta da wannan muguwar dabi’a ba, sai a ‘yan kwanakin nan ne ma a ke tattauna batun don ganin ko zai yiwu a halasta shi ko a haramta.

A tsakankanin shekarar 1970 ne a ka kaddamar da dokar da ke halastawa mara lafiya bijirewa kin aikin likitoci ga cutarshi, wanda kafin nan ko da mutum bai so sai an yi mai aiki matukar ya na fama da ciwo.

Daga wannan ne kuma a ka samu bayyanar ra’ayin neman gudummawa don halaka kai, da kuma halaka mai ciwo don tsananin tausayin halin da ya ke ciki.

Wasu na ganin ya kamata a kaddamar da dokar halascin bayar da gudummawa ga mutum ya kashe kanshi, domin da hakan ne a cewarsu kowa zai samu damar tsara yanayin irin mutuwar da ya ke so.

Wannan ra’ayi bai zo ya samu wuri ya zauna ba, akwai zazzafan martani daga wasu masanan a kan masu yekuwar a halasta dokar, sun ce halasta wannan aiki zai jawo yawaitar alfasha da danyen aiki. Idan a ka ce haka, lallai talauci, rashin aikin yi da kuma fargabar wani abu zai yi ta sa mutane su na neman gudummawar kashe kawunansu.

A ta fannin addini kuwa, masana a ilmin sanin halayyar jama’a da zamantakewa sun tabbatar da illolin wannan aiki, har ma su ka ce mutuwa da rayuwa al’amari ne na Allah, duk wanda ya kashe kanshi saboda wani tsanani ya yi mummunan karshe ne, kuma makomarshi sai ta fi tsananta fiye da tsananin da ya bari a duniya.

Wani shahararren likita da ke zaune a Michigan mai suna Keborkian a tsakankanin 1990 ya yi ta ba marasa lafiya gudummawa su na mutuwa.

Likita Keborkian ya gudanar da wannan aika – aika ne da ta hanyar amfani da wata na’ura mai guba, wacce a ke yiwa lakabi da ‘Death Machine’, akwai wacce ya shirya da zaran mara lafiya ya latsa ta zai halaka.

A Turai ma an yi dirar mikiya a kan likita Keborkian, har ma wasu lauyoyi da ‘yan rajin kare hakkin bil’adama sun yi maka shi a kotu mabambanta, amma alkalai su na kawo tsaiko ga sauraron shari’arshi.

Sai a shekarar 1999 ne wani alkali ya yanke mai hukuncin shekaru 10 zuwa 20 a gidan kurkuku. Haka nan su ma likitoci ‘yan uwan Keborkian sun yi Allah wadai da irin aikinshi.

A Nijeriya ma akwai irin wannan kwamacalar da sunan taimako, musamman ma a jihohin Kudanci.

Wani sashe na Kudancin su na kashe ‘ya ‘ya ne wadanda a ka haifa da cutar Kuturta da ma wasu dangi na nakasar jiki.

A Arewacin Nijeriya ma a na yi, za ka iya tunanin ba haka ba ne, amma kuma hakan ne. A yanzun yankin ya cika ya batse da asibitocin biyuu-ahuu wadanda likitoci ke cin karensu ba babbaka wurin zubar da ciki.

Dubban cikin da likitoci ke zubarwa shi ma gudummawa ce su ke ba wacce (macen) ta ke dauke da cikin da kuma wanda (namijin) ke da alhakin cikin wurin halaka jinjirin da bai ji ba bai gani ba. Idan kin san ba ki so, ko kuma ka san ba ka so, me ya kai ku aikatawa? Mu hadu mako mai zuwa!

Barna
Sulaiman Bala Idris
+ postsBio
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Gwamna Dauda Lawal A Shekara 61:Shugaban Da Ke Gudanar Da Mulki Bisa Kyakkyawar Manufa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    ‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Hayaniya ‘Yar Facebook!
  • Sulaiman Bala Idris
    https://hausa.leadership.ng/author/sulaiman-bala-idris/
    Mummunan Zato

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai

Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.