Majalisar Dokokin Jihar Kogi ta fara aikin sake fasalin dokokin haya na jihar ta hanyar gudanar da sauraron ra’ayoyin jama’a kan wani kudirin doka da aka tsara domin kare masu haya daga karin kudin haya ba tare da ka’ida ba, korar su daga gidaje ba bisa doka ba, da kuma cin zarafin da wasu masu gidaje da dillalan gidaje ke yi.
Sabuwar dokar da ake shirin samarwa na neman soke Dokar Kula da Kudin Haya da Kwato Gidajen Zama ta shekarar 2007, tare da maye gurbinta da Sabuwar Dokar Haya ta Jihar Kogi ta shekarar 2027, wadda za ta dace da yanayin tattalin arzikin yau tare da ƙarfafa haƙƙoƙi da nauyin da ke kan masu gidaje, masu haya da kuma dillalan gidaje.
Kudirin dokar, wanda ɗan majalisar mai wakiltar mazaɓar Ankpa I, Lawal Akus, ya ɗauki nauyi, ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun koke-koke kan tashin farashin hayar gidaje da kuma tsadar kuɗaɗen dillanci a faɗin jihar, musamman sakamakon tsananin matsin tattalin arziki da ake fuskanta a Nijeriya.
Da yake jawabi yayin zaman sauraron ra’ayoyin jama’a, Akus ya ce an kirkiro da kudirin dokar ne domin samar da tsarin doka mai adalci, gaskiya da daidaito wanda zai tafiyar da alakar da ke tsakanin masu gidaje, masu haya da kuma dillalan gidaje a Jihar Kogi.














