ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tsaron Duniya Na Sin Da Na Amurka Wane Ne Ya fi Dacewa Da Muradun Duniya?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A ranar Lahadi ne ministan tsaron kasar Sin Dong Jun ya gabatar da tsarin kasar Sin game da harkokin tsaron duniya a yayin rufe taron tattaunawa na Shangri-La karo na 21 a Singapore, kuma ya gabatar da ra’ayoyin kasar Sin game da warware matsalolin tsaron duniya da mahangar duniya, kana, ya jaddada matsayin kasar Sin kan batun Taiwan, da kuma batun tekun kudancin kasar Sin.

A cikin jawabinsa, janar Dong ya bayyana cewa, manufar kasar Sin na gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga bil’adama, tare da shirin raya kasa da kasa, da shirin samar da tsaro na duniya, da shirin wayewar kai a duniya, ya yi daidai da yanayin tarihi da kuma mayar da martani ga burin mutane a duniya don samun ingantacciyar rayuwa.

  • Sin Ta Kiyaye Zaman Lafiya Da Tsaron Kasa Da Kasa Bisa Ayyukanta Masu Amfani
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 30 Da Kafa CAE

Idan aka kwatanta da jawabin da sakataren tsaron Amurka Lloyd Austin ya gabatar a ranar Asabar, jawabin Dong ya mai da hankali kan batutuwan da suka shafi shiyya-shiyya da ma duniya baki daya, tare da yin la’akari da muradun daukacin bil’adama, shi kuma mista Austin na Amurka ya fi mayar da hankali kan Amurka da kawayenta da abokan huldarta a yankin. Jawabinsa ya ta’allaka ne kawai a kan bukatunsu na son kai da muradun kasarsu, kuma ya yi watsi da kasantuwar ASEAN a cikin batutuwan hadin gwiwar yanki.

ADVERTISEMENT

Jigon jawabin na Austin ya bayyana cewa, Amurka na da burin cimma jagoranci a yankin “Indo-Pacific” ta hanyar tsare-tsare irin su AUKUS, QUAD da sauran kawancen soja, yayin da kuma take wayincewa kan samar da “Indo-Pacific kwatankwacin NATO”. Wanda rashin fahimta ce ta dabara da kuma karkatacciyar fahimtar tsaro da masana suka ce yana haifar da hargitsi da rikici har ma da yaki, maimakon samar da tsaro da kwanciyar hankali.

Bisa la’akari da rikice-rikicen da ke faruwa a Turai da Gabas ta Tsakiya, Asiya Pasifik na daya daga cikin yankuna kadan a duniya da har yanzu ke samun kwanciyar hankali a yau. Masu lura da al’amuran yau da kullun sun ce, a bayyane yake wane tsarin tsaro na duniya, na kasar Sin ko Amurka, ya fi dacewa da muhimman muradu da matsalolin tsaro na galibin kasashen duniya. (Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari’ar Sarakunan Kano

Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari'ar Sarakunan Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.