• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tsaron Duniya Na Sin Da Na Amurka Wane Ne Ya fi Dacewa Da Muradun Duniya?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarin Tsaron Duniya Na Sin Da Na Amurka Wane Ne Ya fi Dacewa Da Muradun Duniya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Lahadi ne ministan tsaron kasar Sin Dong Jun ya gabatar da tsarin kasar Sin game da harkokin tsaron duniya a yayin rufe taron tattaunawa na Shangri-La karo na 21 a Singapore, kuma ya gabatar da ra’ayoyin kasar Sin game da warware matsalolin tsaron duniya da mahangar duniya, kana, ya jaddada matsayin kasar Sin kan batun Taiwan, da kuma batun tekun kudancin kasar Sin.

A cikin jawabinsa, janar Dong ya bayyana cewa, manufar kasar Sin na gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga bil’adama, tare da shirin raya kasa da kasa, da shirin samar da tsaro na duniya, da shirin wayewar kai a duniya, ya yi daidai da yanayin tarihi da kuma mayar da martani ga burin mutane a duniya don samun ingantacciyar rayuwa.

  • Sin Ta Kiyaye Zaman Lafiya Da Tsaron Kasa Da Kasa Bisa Ayyukanta Masu Amfani
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 30 Da Kafa CAE

Idan aka kwatanta da jawabin da sakataren tsaron Amurka Lloyd Austin ya gabatar a ranar Asabar, jawabin Dong ya mai da hankali kan batutuwan da suka shafi shiyya-shiyya da ma duniya baki daya, tare da yin la’akari da muradun daukacin bil’adama, shi kuma mista Austin na Amurka ya fi mayar da hankali kan Amurka da kawayenta da abokan huldarta a yankin. Jawabinsa ya ta’allaka ne kawai a kan bukatunsu na son kai da muradun kasarsu, kuma ya yi watsi da kasantuwar ASEAN a cikin batutuwan hadin gwiwar yanki.

Jigon jawabin na Austin ya bayyana cewa, Amurka na da burin cimma jagoranci a yankin “Indo-Pacific” ta hanyar tsare-tsare irin su AUKUS, QUAD da sauran kawancen soja, yayin da kuma take wayincewa kan samar da “Indo-Pacific kwatankwacin NATO”. Wanda rashin fahimta ce ta dabara da kuma karkatacciyar fahimtar tsaro da masana suka ce yana haifar da hargitsi da rikici har ma da yaki, maimakon samar da tsaro da kwanciyar hankali.

Bisa la’akari da rikice-rikicen da ke faruwa a Turai da Gabas ta Tsakiya, Asiya Pasifik na daya daga cikin yankuna kadan a duniya da har yanzu ke samun kwanciyar hankali a yau. Masu lura da al’amuran yau da kullun sun ce, a bayyane yake wane tsarin tsaro na duniya, na kasar Sin ko Amurka, ya fi dacewa da muhimman muradu da matsalolin tsaro na galibin kasashen duniya. (Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Osimhen A Cikin Tawagar Nijeriya Babbar Asarace – Samson Siasia

Next Post

Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari’ar Sarakunan Kano

Related

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

4 hours ago
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

5 hours ago
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

6 hours ago
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

7 hours ago
Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
Daga Birnin Sin

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

8 hours ago
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

1 day ago
Next Post
Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari’ar Sarakunan Kano

Yajin Aiki Ya Hana Sauraren Shari'ar Sarakunan Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.