Wata mata mai shekaru 28, Firdausi Musa, tare da ‘ya’yanta ƙanana biyu sun samu munanan ƙonewa bayan da ake zargin kishiyarta, Maryam Muhammad, ta zuba musu fetur tare da banka musu wuta a yankin Hotoro da ke cikin birnin Kano.
Lamarin, wanda ya faru a daren Litinin a unguwar Mai Allo da ke Hotoro, ya girgiza mazauna yankin, yayin da ake tsare da wadda ake zargi a ofishin ‘yansanda na Mariri.
Yaran da abin ya shafa, Khadija Ya’u mai shekaru 7 da Ismail Ya’u mai shekaru 3, na samun kulawa tare da mahaifiyarsu a Asibitin Ƙashi na Ƙasa da ke Dala da kuma Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano.
Mijinsu kuma, Malam Saminu, shi ma ya samu ƙonewa yayin ƙoƙarin ceton su daga wutar, inda shi ma yana ci gaba da jinya.
Da yake magana da Daily Trust, ƙanin Firdausi, Buhari Musa Sa’ad, ya ce sun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3 na dare cewa, kishiyar ‘yar uwarsa ta banka wa ‘yar uwarsa da mijinta da yaranta biyu wuta.
A cewarsa, Firdausi ba ta kai makonni biyu da tarewa a gidan mijin ba kafin faruwar lamarin.“Tanada kimanin shekaru 28. Yaran da suka ƙone su ne waɗanda ta zo da su daga aurenta na baya. Su ba ‘ya’yan mijin ba ne, wanda ke aikin tuka adaidaita sahu,” in ji shi.















Discussion about this post