Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75 a gidan yari bayan samun sa da laifin karkatarwa da halasta kuɗaɗen da aka ware domin aikin wutar lantarkida suka kai naira biliyan 33.8.
An same Mamman da laifi a dukkan tuhume-tuhume 12 da Hukumar EFCC ta shigar a kansa.Mai shari’a James Omotosho ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru bakwai a kan tuhume-tuhume 10, yayin da aka yanke masa shekaru uku da shekaru biyu a tuhume-tuhume na huɗu da na biyar bi da bi.
Kotun ta ce za a aiwatar da hukuncin ɗaya bayan ɗaya ba tare da zaɓin biyan tara ba, sai dai tuhume-tuhume na huɗu wanda aka ba da damar biyan tarar naira miliyan 10.
Mai shari’ar ya kuma bayar da umarnin ƙwace kuɗaɗen ƙasashen waje da aka samu daga hannun wanda aka yankewa hukunci, tare da wasu manyan kadarori huɗu masu tsada da ke Abuja da aka danganta su da shi.EFCC ta gurfanar da Mamman a watan Yulin 2024 kan zargin halasta kuɗaɗen haram da haɗa baki da wasu jami’an Ma’aikatar Wutar Lantarki da kamfanoni masu zaman kansu wajen karkatar da kuɗaɗen ayyukan samar da wutar lantarki na Zungeru da Mambilla.
Mamman ya musanta dukkan zarge-zargen da ke cikin shari’a mai lamba FHC/ABJ/CR/273/2024.
A yayin shari’ar, EFCC ta gabatar da shaidu 17 tare da gabatar da hujjoji 43 kafin ta rufe shari’arta.
A ranar 7 ga Mayu, kotun ta same shi da laifi, inda yaki kasancewa a kotu, inda Mai shari’a Omotosho ya ce masu gabatar da ƙara sun tabbatar da zargin ba tare da wata shakka ba.
Daga nan ne kotun ta bayar da sammacin kama shi bayan lauyansa, Mohammed Ahmed, ya bayyana cewa bai san inda wanda yake karewa yake ba kuma duk ƙoƙarin samun sa ta waya ya ci tura.
Bayan yanke hukuncin, alkalin ya umarci hukumomin tsaro su yi haɗin gwiwa da jami’an tsaro na kasa da kasa domin tabbatar da kamo Mamman.
Kotun ta kuma bayyana cewa wa’adin zaman gidan yarin zai fara ne daga ranar da aka kama shi.















Discussion about this post