Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya tattauna ta wayar tarho da ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Sa’ar, bisa bukatar haka da aka gabatar masa.
Bayan ya saurari bayanin da Sa’ar ya yi game da matsayin Isra’ila kan halin da ake ciki, Wang Yi ya bayyana cewa, bangaren Sin ya kasance yana ganin kamata ya yi a warware matsalolin da suka fi jawo hankula a yanki da ma bangaren kasa da kasa ta hanyar tattaunawa da shawarwari, kuma ya kamata dukkan bangarori su bi manufofin da ka’idojin yarjejeniyar MDD. Sin ta dade tana himmatuwa wajen inganta warware matsalar nukiliyar Iran ta hanyar siyasa, kuma tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran kwanan nan tana samun ci gaba sosai, wadda ta hada har da warware matsalolin tsaro na Isra’ila. Abin takaici shi ne, an keta wannan shiri da karfin luguden wuta.
Wang Yi ya ce bangaren Sin yana adawa da hare-haren sojin Isra’ila da Amurka a Iran. Karfi ba zai iya magance matsaloli da gaske ba, illa ya haifar da sababbin matsaloli da cututtuka masu tsanani a yankin. Ma’ana, bai kamata a nuna karfin soja a fagen fama ba, sai dai a bangaren hana yaki.
Wang Yi ya yi kira da a dakatar da ayyukan soja nan take, don hana ci gaba da yaduwar fitinar. Bangaren Sin yana nan a kan matsayinsa na ganin an yi adalci kan batun Gabas ta Tsakiya, kuma zai ci gaba da taka rawar gani wajen sassauta halin da ake ciki.(Amina Xu)















Discussion about this post