Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bukaci a yi dukkan kokari wajen binciko mutanen da har yanzu ba a gansu ba da ceto wadanda suka ji rauni a hatsarin da ya auku a wata masana’antar samar da kayayyakin wasan tartsatsin wuta watau Fireworks.
Hukumomi sun bayyana yayin wani taron manema labarai a yau cewa, lamarin ya auku ne jiya Litinin da rana a wata masana’antar samar da kayayyakin wasan tartsatsin wuta da ke lardin Hunan na tsakiyar kasar Sin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 26 da raunata wasu 61.
Shugaba Xi ya kuma bayar da umarnin karfafa binciken barazana da takaita aukuwar hadura a manyan bangarori, da karfafa aikin kula da aminci da tsaron jama’a da ma kare rayuka da dukiyoyinsu.
Xi ya bukaci a bibiyi lamarin da kyau da kuma gudanar da bincike, yana nanata wajibcin hukunta wadanda alhakin aukuwar lamarin ya rataya a wuyansu.
Ya jaddada cewa, dole ne hukumomi a fadin yankuna da sassa su dauki darasi daga lamarin, su kuma karfafa tabbatar da tsaro da aminci a wuraren aiki.Shi kuma firaministan Sin Li Qiang, ya bukaci a karfafa tabbatar da amincin wuraren aiki a muhimman bangarori da masana’antu da kuma daukar kwararan matakan kare aukuwar hadura. (Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post