Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa yana ganin jam’iyyar ADC ta “mutu”, sakamakon yawaitar ficewar ‘yan majalisa daga cikinta.
Ya faɗi hakan ne a ranar Talata yayin zaman majalisa, bayan sanar da sauya sheƙar wasu sanatoci da ‘yan majalisar wakilai daga ADC zuwa wasu jam’iyyu kamar NDC da Labour Party.
Akpabio ya yi wannan furuci ne cikin yanayin barkwanci, yana mai cewa yawaitar sauya sheƙa ya zama kamar abu na yau da kullum a majalisa.
“Ina ganin ADC ta mutu,” in ji shi, yayin da yake ba da shawarar a rika tattara sunayen masu sauya jam’iyya a lokaci guda maimakon sanar da su ɗaya bayan ɗaya.
Wannan kalamai na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar rikice-rikice na cikin gida a ADC, wanda ya sa wasu ‘yan siyasa ke ficewa daga jam’iyyar zuwa wasu sabbin jam’iyyu gabanin zaɓen 2027.
Kalaman na Akpabio sun nuna yadda wasu jiga-jigan siyasa ke kallon raunin da ADC ke fuskanta a halin yanzu, musamman bayan jerin ficewar da aka gani a Majalisar Tarayya.















Discussion about this post