Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya mika sakon barka da kuma fatan alheri ga ma’aikatan kasar gabanin bikin ranar ’yan kwadago ta duniya, wadda ta fado a ranar 1 ga watan Mayu.
Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS) kuma shugaban kwamitin soja na tsakiya, ya aike da gaisuwar ne a madadin kwamitin tsakiya na JKS.Wannan shekarar ita ce ta cika shekaru 105 da kafa jam’iyyar JKS kuma shekarar farko ta fara aiwatar da shirin bunkasa ci gaban kasa da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15, watau daga 2026 zuwa 2030.
Xi ya yi kira ga ma’aikata a fadin kasar da su yi aiki tukuru tare da samar da sakamako mai kyau, sannan su taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa ci gaban tattalin arziki da zamantakewa mai inganci a matakin koli.Ya kuma jaddada cewa, ya kamata kwamitocin jam’iyya da na gwamnatoci a dukkan matakai su kare hakkoki da muradun ma’aikata bisa doka, kana su magance matsalolin da suka fi addabarsu, sannan su karfafa musu gwiwa domin su kara himmar aiki ba tare da kasala ba don cimma manyan manufofin kasar. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post