Kotun Ƙoli ta umarci ɓangarorin da ke rikici a cikin jam’iyyar ADC da su koma Babbar Kotun Tarayya domin ci gaba da shari’ar da Bala Gombe ya shigar kan shugabancin jam’iyyar.
Kotun ta kuma soke hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke wanda ya umurci ɓangarorin da su ci gaba da zama a yadda al’amura suke kafin rikicin ya ɓarke (status quo ante-bellum).
A cewar Kotun Koli, hukuncin da ya dace shi ne a mayar da shari’ar zuwa Babbar Kotun Tarayya domin a saurare ta yadda ya kamata, maimakon bayar da umarnin ci gaba da matsayin da ake ciki.
Sai dai kotun ta yi watsi da wani ɓangare na ƙarar ɗaukaka ƙarar bisa dalilin cewa tana da matsala ta doka.
Ta bayyana cewa ƙarar da jam’iyyar ADC ta shigar ba ta cika sharuɗɗan doka ba, domin ba a nemi izinin kotu ba kafin shigar da ita.
Kotun ta jaddada cewa neman izinin kotu muhimmin sharaɗi ne kafin a shigar da ƙarar ɗaukaka ƙara, don haka ta bayyana ƙarar a matsayin mara inganci da rashin ƙwarewar doka.















Discussion about this post