• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini

by Dokta Nasir Aminu
2 years ago
in Bakon Marubuci
0
Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun lokacin da aka sanya hannu a dokar zabe da ake yi wa kuskwarima ta shekarar 2022 har ta zama doka, mutane suka fara hasashen cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) za ta iya gudanar da ingantaccen zabe wanda ba a taba irinsa ba a tarihin Nijeriya.

Ko da ma aka samu rahoton rashin tsaro zai iya sanyawa a dage zabe bai sauya tunanin shugaban hukumar ba. Mutane ma dai sun san cewa wannan ba huruminsa ba ne, akwai dan abu kadan da hukumarsa za ta iya yi.

  • Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro
  • NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai

Hukumar tana da wasu kalubale a tsare-tsarenta, amma wadannan matsaloli an magance su kuma zai iya faruwa a kowani lokaci, kuma a kowacce kasa. Matsalar da ake fama da shi wanda ya kamata INEC ta duba shi ne, yadda ‘yan siyasar Nijeriya suke zuzuta dabi’ar nan ta siyasar kabilanci da addini.

Sashi na 97 na dokokin zaben shekara ta 2022, ya zayyano cewa haramun ne yin yakin neman zabe a kan addini ko kabila. Dokar ta ce: duk dan takara koko wani mutum ko wata kungiya suka yi yakin neman zabensu a kan addini ko kabilanci ko bangaranci don sun tallata jam’iyyarsu ko su soki wani bangare ko dan takara sun aikata laifi a karkashin wannan sashi(a), wanda zai biya mafi yawan kudi na Naira miliyan 1,000,000 ko kuma a daure shi a gidan yari na tsawon shekar 12 ko kuma a hada mashi su gaba daya, sashi (b) idan kuwa jam’iyyar siyasa ta aikata wannan za ta biya mafi yawan kudi na Naira miliyan 10,000,000.

Wannan matsalar a nan idan aka danganta da jam’iyyar APC, wadanda suke amfani da wannan dama na cewa sun bayar da tikitin takararsu ga wadanda suke addininsu guda. A dokance kowa zai iya zabar wadanda suke addini guda don ma an yi a baya can, kenan wannan ba sabon abu ba ne. Zaben da aka soke na shekarar 1992 an yi tikitin musulmi da musulmi, inda Abiola da Kingibe suka yi takara a karkashin jam’iyyar SDP. Kafin takarar MKO, akwai takarar da aka yi na Kirista da Kirista a jamhoriya ta biyu a shekarar 1979, inda Cif Awolowo ya tsaya takara da abokin takararsa, Philip Umeadi, sai kuma Azikiwe na jam’iyyar NPP da abokin takararsa, Ishaya Audu. Dukkaninsu sun tsaya takara inda Shagari da Ekwueme da suke da tikitin musulmi da Kirista suka sami nasara.

Labarai Masu Nasaba

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

Waraka Daga Bashin Ketare

Wannan tataburza na maganar tikitin musulmi da musulmi ya fara tashe ne a shekarar 2019, inda ya taso a matakin Jihar Kaduna. Tsarin dai jam’iyyar gwamnati ce ta tsara shi karkashin jagorancin El-Rufa’i don samun wata daman a kasancewar jihar musulmai sun fi yawa. Wannan ne ya haifar da sauya al’adar jihar na hada musulmi da kirista takara, inda aka koma tikitin musulmi da musulmi a Kaduna wanda hakan ya kara matsalar rashin tsaro. Duk da kiraye-kiraye mabambanta da ake ta yi a kan haka, amma jam’iyyar gwamnati ta yi watsi da wannan kiran, ba don komai ba sai don suna da son su sami nasarar zabe.

Lallai kuwa ‘yan siyasa suna yin tunanin daukan duk wani mataki da zai kai su ga nasara ba sa tunanin me zai dawo. Amma abun da yake nunawa karara shi ne ba sa tunanin talakawa da suke mulka kuma su ne masu zabe, bukatarsu shi ne samun nasara, misali a dauki Jihar Kaduna inda ake fama da matsalar tsaro wanda ya karu sakamakon amfani da addini. Darasin da ya kamata a dauka shi ne, yana nuna cewa duk da cewa yin tikitin musulmi da musulmi bai saba wa doka ba, amma a duba yanayin mutanen da suke zama a wurin.

Yin tikitin musulmi da musulmi ya sanya damuwa a zukatan kungiyoyin Kiristoci da suka hada da ita kanta CAN. Damuwar ita ce samun nasarar jam’iyyar APC yana da matukar wahala sakamakon mabiya addinin kirista da aka nuna masu cewa ba su isa ba, kuma mutane da dama suna tunanin tarihi ne zai maimaita kansa a kan abun da ya faru a shekarar 1979, inda wadanda suka tsayar da masu addini daya suka sha kaye.

Matsalar da aka samu shi ne, yadda wasu kiristoci suka ce su kuma nasu za su goyawa baya, wato Peter Obi. Wannan ya zo na bazata ko kuma tsararren shiri ne, amma kamar matakin bai karbu ba. Wata ziyara da Peter Obi ya kai coci an ji yana rokon mahalartar cocin da cewa su farka daga barci don su karbo kasarsu. A lokacin yakin neman zabe a Filato, wani Fasto ya ya yi kira ga kiristoci da su zo su karbi kasarsu. Wannan ma ya zama sababben sako, amma sakon ana daukansa karmar yanki-yanki ne wanda yake cikin ajandan al’ummar musulmi.

A bangarensu kuwa kungiyar Izala a wani taro da suka yi da gwamna Ganduje na Jihar Kano don su nuna goyon bayan tikitin musulmi da musulmi. Wani malami ya bayyana a cikin wani faifan bidiyo yana cewa tikitin musulmi da musulmi ya fi tikitin musulmi da kirista, sun fi mayar da hankalinsu kan tikiti ba wai matsalar tattalin arzikin kasa ba. Wani faifan bidiyo da aka yada da ke dauke da malamai suna taro, inda suke cewa zaben musulmi da musulmi kamar jihadi ne.

Dukkanin addinan nan suna zargin junansu kamar tsarin nan na karba-karba. Yakin neman zabe a kan addini iri daya ne, malamai da jagororin addini suna kiran magoya bayansu a kan su zabi wanda suke addini guda da su. Malamai da ‘yan siyasa suna magana ne a karan kansu ba sa duba alfanun jama’a kuma hakan da suke yi ya saba wa sahi na 97 na dokar zaben shekara ta 2022.

Idan aka yi la’akari da faya-fayan bidiyon da ake yadawa, ya zama wajibi hukumar INEC ta hukunta wadanda suka karya dokar. Kuma hukuncin wanda ya karya dokar an tanaje shi a karkashin dokar, kuma hakan zai sa a daina karya dokar. Abun mamaki sai INEC ta kawar da idonta a kan wannan. Shirun da ta yi yana nuna cewa INEC ko ta amince a karya dokar ko kuma ba ta san abun da dokar sahi na 97 yake nufi ba.  Koma dai mene ne wannan bai kyautu ba ga hukumar. Ya kamata ta samar da dukkanin abubuwan da ake bukata wajen gudanar da zabe.

Jam’iyyun adawa sun fito fili sun bayyana abubuwan da ya shafe su. Jam’iyyu da suka shirya sun gudanar da ingantaccen yakin neman zabe don su sami kuri’a ba wai don su yi amfani da wata dama ba don kawar da tunanin masu zabe ta hanyar amfani da addini. Kamar Peter Obi ko Tinubu suna amfani da addini wajen yakin neman zabe.

Jam’iyyu da suke yakin neman zabensu a bisa al’adar da ake yi a baya na tikitin musulmi da kirista, kamar Jam’iyyar PDP za ta iya samun dama da matakan da wadannan suka dauka wanda hakan ya rarraba kuri’unsu.

A saboda haka, ya zama wajibi hukumar INEC ta yi hukunci ga duk wadanda suke karya doka ba don komai ba sai don ganin an sami ingantaccen zabe kuma karbabbe idan an sami tsaro. Idan ba haka kuwa, mutuncin hukumar da kuma na Buhari zai zube.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AddiniINECYakin Neman ZabeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Messi Ya Fi Maradona A Argentina –In Ji Kocinsa

Next Post

Ina Koyi Da Dabi’un Muhammad Ali – Pogba

Related

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

4 weeks ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

1 month ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

2 months ago
Next Post
Ina Koyi Da Dabi’un Muhammad Ali – Pogba

Ina Koyi Da Dabi’un Muhammad Ali - Pogba

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.