ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Inganta Tsarin Harkokin Kudi Na Dattawa A Kasar Sin

by Sulaiman
6 months ago

Sin a matsayin kasa mai tafiya a kan turbar fifita rayuwar al’umma, tana kara mai da hankali kan inganta tsarin yadda dattawa za su rika tafiyar da sha’anin kudadensu, yayin da take kara kimtsa wa karuwar adadin mutanen da ke tsufa. Bisa yadda take da adadin fiye da mutane miliyan 310 masu shekaru 60 zuwa sama, da kuma fiye da miliyan 45 masu bukata ta musamman, kasar ta himmatu wajen inganta tsarin kudi mai nagarta ga dattawa.

A duk fadin kasar, larduna da biranen suna fitar da sabbin tsare-tsare don inganta harkokin kudi su zama masu sauki ga dattawa. Misali, lardin Guangdong ya bullo da matakai 15 don gina wani tsarin hada-hadar kudi na dattawa a lardin nan da shekarar 2028. Manufar hakan ita ce samar da ingantacciyar hanyar zuba kudade a cikin asusun fansho da kuma kyautata muhimman ayyukan kula da dattawa.

Sauran yankuna kamar Jilin, Chongqing, da Qingdao su ma suna kara mayar da hankali kan wannan, inda Qingdao ta kaddamar da wani shiri na shekaru uku wanda ke sada ayyukan hidimomi na kudi da inshorar kiwon lafiya, da harkokin jama’a, da kuma kula da dattawa. Jilin kuma tana karfafa gwiwar masu gudanar da al’amuran inshora wajen ganin sun fadada nau’o’in ayyukansa da kuma habaka ba da kariya ga kudaden dattawa.

ADVERTISEMENT

Wadannan matakai da yankunan kasar Sin ke daukawa sun zo a kan gaba, musamman bisa karuwar yawan dattawa kuma duk da yawancin dattawan yanzu suna da karfin aljihu da sababbin dabaru na tsimi da tanadi da kuma amfani da kudadensu, amma suna bukatar tsarin da zai sada sha’aninsu na kudi da ayyukan kiwon lafiya, da harkokin nishadi, da kuma more rayuwarsu a manyan wuraren kulawa da dattawa.

Wani bincike na baya-bayan nan da aka gudanar ya nuna cewa kashi 70 cikin 100 na wadanda aka ji ta bakinsu sun nuna bukatar ganin bankuna suna taimakawa wajen samun ayyukan kiwon lafiya cikin sauki, yayin da kusan kashi 60 cikin 100 kuma suke sha’awar ganin an sada tsakanin harkokinsu na kudi da kuma wuraren kula da rayuwar dattawa.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Bankunan sun fara duba wannan bukata, inda yanzu haka Bankin CCB na kasar Sin ya muhimmanta ba da fifiko ga dattawa a tsare-tsarensa na bayar da bashi, yayin da Bankin masana’antu kuma ya fitar da wata takardar bayani da ke bayyana karin kebabbun hidimomin kudi ta amfani da shafin intanet da sauran hanyoyi na zabi da suka shafi kula da sha’anin dattawa.

Sakon hakan dai a bayyane yake, ma’ana, cire fargaba kan sha’anin kudin dattawa da kuma samar da ingantattun tsare-tsare masu tallafa wa rayuwar dattawa ta hanyar samun koshin lafiya, da aminci mai gamsarwa a shekarunsu na tsufa.

Tabbas, a yayin da kasar Sin ke dab da fara aiwatar da shirin bunkasa ci gaban kasa da zamantakewar al’umma na shekaru biyar-biyar karo na 15, nasarar wadannan tsare-tsare za ta taka muhimmiyar rawa wajen tsara makomar kula da kudaden dattawa yadda ya kamata. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
AFCON 2026: Algeria Ta Lallasa Sudan Da Ci 3 Da Nema

AFCON 2026: Algeria Ta Lallasa Sudan Da Ci 3 Da Nema

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.