Dangane da batun mayar wa kasar Sin da kayan tarihi da Amurka ta yi, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun, ya yi tsokaci a wani taron manema labarai na yau da kullum a yau 18 ga watan nan, yayin da yake amsa tambayar da wani dan jarida ya yi masa, inda ya bayyana cewa, wannan mataki na mayar da kayan shi ne sakamako na baya-bayan nan game da aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a yayin ganawarsu a birnin Beijing.
Hakan kuma ya nuna kyakkyawan fata game da gina dangantaka mai inganci cikin kwanciyar hankali bisa manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Amurka.
A cewar rahotanni dai, hukumar kula da al’adun gado ta kasar Sin ta karbi wasu rukuni biyu na kaya da suka kunshi jimillar kayayyakin tarihi 64 ko kuma saitinsu, da ayyukan fasaha, da burbushin halittun da suka dade da bacewa, wadanda Amurka ta mayar wa kasar Sin ta hannun hukumar bincike ta ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurka da ofishin babban lauyan yankin Manhattan, a biranen Washington da New York a ranakun 16 da 17 ga watan nan agogon kasar. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)













