ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Kasar Sin Ke Tasiri A Duniya

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Idan muka ce duniya baki daya ta bibiyi sanarwar cikakken zaman taro karo na 3 na kwamitin kolin JKS karo na 20 ba mu yi karya ba. Magoya baya da abokan huldar Sin sun kasa kunne su ji tabbacin labarin kwanciyar hankali da daidaiton tsarin ci gaban kasar, yayin da masu sukar lamirin kasar suka yi ta kokarin gano alamun karuwar matsaloli, da damuwa, ko ma yiwuwar rarrabuwar kawuna tsakanin shugabannin JKS. A karshe dai, magoya baya sun samu dalilan da suka kwantar musu da hankali, kuma masu zagi dole ne su kasance cikin takaici. A bayyane, zaman ya nuna ci gaba a tsarin siyasa, da tattalin arziki da zamantakewa da aka tsara a babban taron JKS karo na 20 da aka gudanar a shekarar 2022. Zaman ya mayar da hankali ne kan al’amuran cikin gida da nufin kammala aikin zamanantarwa bisa tsarin gurguzu nan da shekarar 2035, da gina ingantacciyar hanyar tattalin arziki ta gurguzu da kuma zamanantar da tsarin kasar da iya tafiyar da harkokin mulki.

Mu dubi tsarin kasuwancin duniya na wannan zamani, jimillar kayayyakin shige da fice na kasar Sin ya kai kusan dalar Amurka tiriliyan 6, lamarin da ya sa kasar Sin ta kasance babbar abokiyar cinikayya ga kasashe fiye da 120. Kasar Sin tana da fiye da rabin sabbin motocin lantarki da aka sayar a duk duniya a yau, kuma tana daukar sama da kashi 80 cikin 100 na kayayyakin samar da wutar lantarki bisa hasken rana a duniya. Yana da wuya a yi tunanin kasuwannin duniya na kwamfutoci da na’urorin laturoni, da sinadarai na hada magunguna, da injuna, da motoci, da sauran kayayyaki daban-daban ba tare da tabo rawar da kasar Sin ta taka ba.

Kusan shekaru 100 da suka shige, tsohon shugaban Amurka Franklin D. Roosevelt ya bayyana cewa, “Yadda matsayinmu a tarihi ke cike da haske haka yake da hadari. Ko dai duniya ta karkata zuwa ga ci gaba da hadin kai da wadatar arziki a ko’ina, ko kuma ta rarrabu.” Wannan gaskiya ne a shekarun 1930s kuma ba shakka haka lamarin yake a zamaninmu na yau. Dukkanmu masu ruwa da tsaki ne wajen samun nasarar ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin saboda hakan na da matukar tasiri ga tattalin arzikin duniya. Kuma wadanda ke yi wa Sin munanan fata harbin kansu kawai suke yi a kafa. (Mohammed Yahaya)

ADVERTISEMENT
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin
  • Sulaiman
    NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 27 A Sansanonin Tumbus Na Borno
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

MASU ALAKA

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Daga Birnin Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

June 14, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Wata Ƴar Chibok, Sun Miƙa Ta Ga Gwamnatin Borno

Sojoji Sun Ceto Wata Ƴar Chibok, Sun Miƙa Ta Ga Gwamnatin Borno

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 27 A Sansanonin Tumbus Na Borno

June 14, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna

Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.