Rashin jin shawara: Akwai wasu mutane da ba sa karɓar nasiha ko gyara, duk yadda aka yi ƙoƙarin shiryar da su. Irin waɗannan mutane suna buƙatar addu’a da ci gaba da yi musu nasiha cikin hikima.
Hanyoyin magance matsalar:
Kyakkyawar tarbiyya daga iyaye:
Ya kamata iyaye mata su zama abin koyi ga ƴaƴansu. Su koya musu girmama mutane, kyautata mu’amala da abokan zama da kuma fahimtar cewa zaman lafiya da haƙuri su ne ginshiƙan zaman aure.
Bawa taarbiyya muhimmanci a makarantu:
Makarantu su ƙara ba da muhimmanci ga tarbiyya tare da ilimi domin a gina ɗalibai masu kyawawan ɗabi’u da mutunta hakkin wasu.
Gaskiya da riƙon amana ga mazaje:
Ya kamata maza su guji yin alkawurran da ba su da tabbacin cikawa. Gaskiya da riƙon amana su ne tushen zaman lafiya a aure.
Adalci tsakanin mata:
Mazaje su yi iya ƙoƙarinsu wajen tabbatar da adalci tsakanin matansu, domin adalci yana rage fitina kuma yana ƙarfafa zaman lafiya.
Tsoron Allah:
Mace ko namiji ya kamata ya tuna cewa duniya mai wucewa ce, kuma kowa zai tsaya a gaban Allah domin hisabi. Tsoron Allah yana hana zalunci, hassada da sauran munanan ɗabi’u.
Zafin kishi na daga cikin matsalolin da ke kawo rikice-rikice a gidajen aure da cikin al’umma baki ɗaya. Don haka akwai buƙatar iyaye, malamai, ma’aurata da sauran jama’a su haɗa hannu wajen gina tarbiyya mai kyau, yin adalci da kuma tsoron Allah.
Allah ya sanya mu cikin bayinsa masu kyawawan ɗabi’u, ya kuma tsare zukatanmu daga hassada, ƙyashi da zafin kishi. Ameen.













