ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada
1 hour ago
Spain

Hukumar kwallon kafa ta Duniya FIFA, ta karrama wasu gwarazan ‘yanwasa biyar da suka yi fice a gasar Kofin Duniya ta 2026 da aka kammala a ranar Lahadin da ta gabata.

A kowace Gasar Kofin Duniya da FIFA ke shiryawa takan lura da wasu ‘yanwasan da suka fi fice a fannoni daban-daban domin karrama su kan rawan da suka taka a gasar.

Sifaniya ce ta lashe kofin bayan doke Argentina – wadda ta dauka a 2022 – da ci 1-0 a wani wasa da ya dauki hankalin masoya kwallon kafa a fadin duniya. Karo na biyu kenan da Spain ke daukar kofin bayan wanda ta dauka a gasar 2010 da aka gudanar a kasar Afirka ta Kudu.

ADVERTISEMENT

‘Yan wasa biyar da FIFA ta karrama bayan kammala gasar Kofin Duniyar su ne:

RODRI

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Dan wasan tsakiya na Sifaniya ya lashe kyautar Golden Ball, wadda ake bai wa gwarzon dan wasa a gasar baki daya. Kyaftin din tawagar Sifaniyan ya kasance jigon tsakiyar fili, inda ya taimaka wa kasarsa wajen sarrafa wasanni da kuma kaiwa ga lashe kofin duniya ba tare da rashin nasara ba.

Dan wasan tsakiyar na Manchester City ya kware wajen sarrafawa da rarraba kwallo a tsakiyar fili. Rawar da ya taka ta sa aka dauke shi a matsayin mafi tasiri a gasar.

MBAPPE

Kylian Mbappé na Faransa ne ya lashe kyautar danwasan da ya fi zura kwallo a raga, wadda ake kira ‘Golden Boot’ da FIFA ke bayarwa. Dan wasan gaban na Real Madrid ya zura kwallo 10 a gasar, inda ya kare a gaban Messi na Agentina mai takwas. Banda  bajintar zura kwallaye a gasar 2026, Mbappé ya kafa tarihin danwasan da ya fi zura kwallaye a tarihin gasar Kofin Duniya, inda ya ci 22.

Duk da cewa Faransa ba ta kai wasan karshe ba, Mbappé ya nuna bajinta wajen cin kwallaye a kusan kowane mataki na gasar.

UNAI SIMÓN (SIFANIYA)

Unai Simón mai tsaron ragar Sifaniya ne ya lashe kyautar Safar Zinare ta mai tsaron raga mafi kwazo a gasar Kofin Duniya ta 2026. Simón ya taka muhimmiyar rawa wajen taimaka wa Spain, inda ya yi wasanni bakwai ba tare da kwallo ta shiga ragarsa ba.

Kuma a duka tsawon gasar sau daya ne kawai kwallo ta shiga ragarsa.

PAU CUBARSÍ (SIFANIYA)

Pau Cubarsí na Sifaniya ne ya lashe kyautar matashin danwasan mafi kwazo a gasar.

Mai tsaron bayan ya nuna jajircewa wajen tsaron bayan Sifaniya a daukacin gasar, inda ya buga duka wasannin kasar takwas a gasar. Dan wasan mai shekara 19, da ke buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ya haska sosai duk da karancin shekarunsa a gasar.

NETHERLANDS

Kyauta ta karshe ita ce wadda aka bai wa Netherlands a matsayin wadda ta fi nuna kyawawan dabi’u a gasar. FIFA ta ce Netherlands ta nuna kyakkyawar dabi’a da ladabi da mutunta dokokin wasa a tsawon gasar. Bayanai sun ce katin gargadi uku kawai aka bai wa tawagar, yayin da ba ta yi wani laifin da ya cancanci katin kora ba.

Duka katin gargadin uku na Netherlands ta same ne a wasan farko da ta buga da Japan. Bayan haka ba ta kara samun katin gargadi ba a duka sauran wasannin nata, har zuwa lokacin da Moroko ta fitar da ita a matakin ‘yan 32.

Spain
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?
  • Abba Ibrahim Wada
    Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?
Wasanni

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032
Wasanni

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC
Wasanni

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026
Next Post
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Spain

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Spain

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.