Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe mutum daya tare da sace wasu 11 a unguwar Gadanaji da ke Karamar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna.
A cewar majiyoyin yankin, harin ya faru ne da tsakar dare a ranar Alhamis, da misalin karfe 1:44, lokacin da fiye da ’yan bindiga 20 dauke da makamai suka mamaye unguwar, suna harbe-harbe ba kakkautawa tare da jefa mazauna yankin cikin firgici.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, afkowar ‘yan bindigar ba-zato-ba-tsammani, ta tayar da hankulan al’ummar, lamarin da ya tilasta musu guduwa daga gidajensu cikin rudani yayin da suke kokarin tsira daga harin.
Da yake tabbatar da harin, Faston Cocin Katolika na St. John Paul II da ke Gadanaji, Rev. Fr. Francis Ezeokwelume, ya ce, maharan sun dauki lokaci mai tsawo suna aikata ta’asarsu ba tare da wata tsangwama ba, inda suka gudanar da sace-sacen tare da kwashe kayayyaki masu daraja.















Discussion about this post