Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi Allah-wadai da kisan Ibrahim Khalil, wanda aka fi sani da Danshagamu, mai sharhin siyasa da amfani da kafafen sada zumunta.
A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Laraba, Gwamna Yusuf ya umarci jami’an tsaro da su gudanar da bincike domin gano waɗanda ake zargin suna da hannu a kisan tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin abin damuwa, yana mai cewa ya kamata a gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da cewa duk wanda ke da hannu a kisan ya fuskanci hukuncin da doka ta tanada.
Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, abokansa da abokan aikinsa, tare da addu’ar Allah Ya gafarta masa, Ya jiƙansa da rahama, Ya kuma ba shi makoma mai kyau.
Gwamna Yusuf ya yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankalinsu tare da guje wa ɗaukar doka a hannunsu. Ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da aiki tare da jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma umarci hukumomin tsaro, musamman DSS da Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta Jihar Kano, da su ƙara ƙaimi wajen binciken lamarin, gano tare da kama waɗanda ake zargi da hannu a kisan, domin gurfanar da su a gaban kotu.














