Kwamishinan ’yansandan Jihar Sakkwato, Hayatu Shafa, ya gargaɗi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su guji tashin hankali, kalaman ƙiyayya, yaɗa labaran ƙarya da sauran abubuwan da ka iya kawo cikas ga zaɓen 2027.
Kwamishinan ya yi wannan gargaɗin ne ranar Laraba yayin wani taro da shugabannin da wakilan jam’iyyun siyasa a jihar.
Ya buƙaci jam’iyyun da su gudanar da yaƙin neman zaɓe cikin lumana tare da yin aiki da hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa zaɓen ya gudana ba tare da tashin hankali ba.
Shafa ya ce zaɓen 2027 ya kamata ya kasance bisa ra’ayoyi, ba yaƙi ba, kuma a bar masu zaɓe su zaɓi shugabanninsu cikin ’yanci.
Ya kuma bukaci ’yan siyasa su guji yaƙin neman zaɓe mai cike da zagi, yaɗa labaran ƙarya da ɓata sunan abokan hamayya.
A maimakon haka, ya ce su mayar da hankali kan manufofinsu da shirye-shiryensu ga al’umma.
Kwamishinan ya gargaɗi shugabannin jam’iyyun cewa za a ɗora musu alhakin duk wani rashin ɗa’a da magoya bayansu suka aikata, ciki har da ƙungiyoyin matasa da masu tasiri a kafafen sada zumunta.
Ya ce ’yansanda za su yi amfani da Dokar Zaɓe ta 2022 wajen hukunta duk wanda ya karya dokokin zaɓe.
Haka kuma, ya buƙaci jam’iyyun siyasa su riƙa bai wa hukumomin tsaro bayanai kan barazanar tsaro ko wuraren da ake ganin za su iya fuskantar tashin hankali.
Shafa ya kuma gargaɗi ’yan siyasa da ka da su jefa masu zaɓe cikin hatsri a yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga, musamman Sabon Birni, Rabah, Kebbe, Tureta da Isa.













