Da yammacin yau Alhamis, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugabar kasar Namibiya Netumbo Nandi-Ndaitwah a birnin Beijing, yayin da take ci gaba da ziyarar aiki a kasar.
Yayin zantawar ta su, Li Qiang ya ce Namibia muhimmiyar abokiyar hulda ce ta kasar Sin a nahiyar Afirka. Kuma a shekarun baya bayan nan, bisa hadin gwiwar sassan biyu, alakar Sin da Namibia ta ci gaba da zurfafa, kuma bisa hadin gwiwa na hakika, sun kai ga cimma jerin sabbin nasarori, da amfanar da al’ummun kasashen biyu.
Kazalika, Li Qiang ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tare da Namibia, wajen daga matsayin kawancen gargajiya, da karfafa goyon bayan juna kan muhimman kudurorinsu, da manyan abubuwan da suke mayar da hankali a kai, da yayata hadin gwiwar cimma moriyar bai daya, don kara zurfafa da inganta zamanantar da kasashen biyu.
A nata bangaren kuwa, shugaba Ndaitwah, cewa ta yi Namibia na nacewa manufar kasar Sin daya tak a duniya, tana kuma fatan yin aiki tare da Sin wajen cimma gajiyar manufar kawar da dukkanin haraji da Sin ta ayyana, da kara zurfafa hadin gwiwa a karin sassa, kamar cinikayya, da noma, da hakar ma’adanai, da samar da ababen more rayuwa, da sufuri da safarar hajoji.
Sauran sun hada da fannin kiwon lafiya, da makamashin da ake iya sabuntawa da sauransu.Har ila yau, tana fatan sassan biyu za su karfafa musayar al’adu, a fannoni irinsu yawon bude ido, da ilmi, da hadin gwiwa tsakanin matasa.
Shugabar ta Namibia, ta kuma yi fatan za a kai ga cimma manyan nasarori, da haifarwa al’ummun kasashen biyu babbar gajiya, karkashin cikakken kawance bisa manyan tsare-tsare tsakanin Namibia da Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)













