• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Nemi Gwamnati Ta Bunkasa Kiwon Dabbobi A Kasar Nan – Lawan

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Adalci Ne Kadai Zai Ce Ci Nijeriya, Inji Lawan Da Saraki Da Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, ya sha alwashin cewa zauren majalisar dattawan Nijeriya zai yi kokarin tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta tallafawa harkokin kiwon dabbobi a kasar nan- a matsayin sa na daya daga cikin manyan ginshikan ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Sanata Lawan ya sanar da hakan a karshen mako, a sa’ilin da yake kaddamar da allurar riga-kafi ga dabbobi kyauta a kauyen Jajuwa dake karamar hukumar Jakusko a jihar Yobe; shirin da Gidauniyar SAIL Foundation a karkashin sa ke daukar nauyin gudanar dashi tun shekarar 2018, domin al’ummar mazabar sa.

  • Adalci Ne Kadai Zai Ce Ci Nijeriya, Inji Lawan Da Saraki Da Wike

Ya ce harkokin kiwo a Nijeriya ba kashin yasarwa bane, a matsayin sa na daya daga cikin manyan kadarkon da ke dauke da tattalin arzikin Nijeriya, “wanda kuma ya dace gwamnati ta tallafa wa harkar kiwo, saboda muke cin gajiyar fanni wajen ci gaban tattalin arzikinmu, sannan barin sa haka ba tare da agaza wa bangaren ba, to ba a yi masa adalci ba; duk sana’a ce mai zaman kanta, dole a tallafa wa sashen.”

 

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

“A hannu guda kuma, suma bankuna harkar sana’a ce mai zaman kanta, wanda idan har gwamnati za ta tallafa wa masu tafiar dasu ba, ban ga dalilin da za a ki tallafa wa makiyaya dabbobi ba, wanda a zahiri ma sune suka fi kowa cancanta a tallafa musu, musamman gwamnatin tarayya.”

 

Sanata Lawan ya kara da cewa, “Zamu ci gaba da matsa wa Gwamnatin Tarayya lamba har sai ta tallafawa Fulani makiyaya dabbobi domin rage matsalolin da su ke fama da su lokaci zuwa lokaci.”

 

“Sannan a kokarinmu, a yau mun zo nan ne domin kaddamar da allurar rigakafin dabbobi, wadanda suka kunshi shanu, tumaki, da awakinmu, tare da sauran kananan dabbobi a wannan shiyya ta Yobe ta Arewa.”

 

“Wannan biki ne wanda muke gudanar dashi kowace shekara domin yiwa dabbobi allurar riga-kafin cutuka daban-daban, wanda a bara mun yi wa dabbobi kimanin miliyan daya da rabi, kuma a wannan shekara ma haka zamu yi. Sannan zamu kara da bai wa Fulaninmu tallafin dusa da sauran abincin dabbobi kyauta, domin rage musu wahalhalu.”

 

Bugu da kari, Sanata Lawan ya kaddamar da shirin bai wa al’ummar yankin sa tiyata kan matsaloli daban-daban kyauta, wanda ake gudanar dashi tun shekaru biyar da suka gabata, a asibitin kwararru na jihar Yobe dake Gashua, da Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) ta Nguru.

 

Ya ce tallafin ayyukan jinya kyauta domin masu fama da rashin lafiyar ido, tiyata kaba, duba lafiyar mata da yi wa wasu tiyata, gwajin cutar dadji, da sauran su, duk a kyauta ga kimanin mutum 5000.

 

Har wala yau, Sanata Lawan ya yi alkawarin gina Cibiyar kula da masu fama da cutar koda a Asibitin Kwararru ta Gashuwa domin saukake wa jama’ar yankin wahalhalun cutar. Kana da sake gyara hanyar Kwanar-Baderi zuwa Gir-gir, hanyar mota tare da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a sabuwar Sakandare Gwamnatin Tarayya dake Gashuwa, da sauran muhimman ayyuka a ziyarar da ya kai ta kwanaki uku a Yobe ta Arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin CCECC Na Sin Zai Gina Kasuwar Zamani A Addis Ababa

Next Post

Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin ‘Yan Ta’adda Da Ke Kaduna

Related

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

27 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

10 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

11 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

13 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

14 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

15 hours ago
Next Post
Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin ‘Yan Ta’adda Da Ke Kaduna

Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin 'Yan Ta'adda Da Ke Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.