ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Nemi Gwamnati Ta Bunkasa Kiwon Dabbobi A Kasar Nan – Lawan

by Muhammad Maitela
4 years ago
Lawan

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, ya sha alwashin cewa zauren majalisar dattawan Nijeriya zai yi kokarin tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta tallafawa harkokin kiwon dabbobi a kasar nan- a matsayin sa na daya daga cikin manyan ginshikan ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Sanata Lawan ya sanar da hakan a karshen mako, a sa’ilin da yake kaddamar da allurar riga-kafi ga dabbobi kyauta a kauyen Jajuwa dake karamar hukumar Jakusko a jihar Yobe; shirin da Gidauniyar SAIL Foundation a karkashin sa ke daukar nauyin gudanar dashi tun shekarar 2018, domin al’ummar mazabar sa.

ADVERTISEMENT
  • Adalci Ne Kadai Zai Ce Ci Nijeriya, Inji Lawan Da Saraki Da Wike

Ya ce harkokin kiwo a Nijeriya ba kashin yasarwa bane, a matsayin sa na daya daga cikin manyan kadarkon da ke dauke da tattalin arzikin Nijeriya, “wanda kuma ya dace gwamnati ta tallafa wa harkar kiwo, saboda muke cin gajiyar fanni wajen ci gaban tattalin arzikinmu, sannan barin sa haka ba tare da agaza wa bangaren ba, to ba a yi masa adalci ba; duk sana’a ce mai zaman kanta, dole a tallafa wa sashen.”

 

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

“A hannu guda kuma, suma bankuna harkar sana’a ce mai zaman kanta, wanda idan har gwamnati za ta tallafa wa masu tafiar dasu ba, ban ga dalilin da za a ki tallafa wa makiyaya dabbobi ba, wanda a zahiri ma sune suka fi kowa cancanta a tallafa musu, musamman gwamnatin tarayya.”

 

Sanata Lawan ya kara da cewa, “Zamu ci gaba da matsa wa Gwamnatin Tarayya lamba har sai ta tallafawa Fulani makiyaya dabbobi domin rage matsalolin da su ke fama da su lokaci zuwa lokaci.”

 

“Sannan a kokarinmu, a yau mun zo nan ne domin kaddamar da allurar rigakafin dabbobi, wadanda suka kunshi shanu, tumaki, da awakinmu, tare da sauran kananan dabbobi a wannan shiyya ta Yobe ta Arewa.”

 

“Wannan biki ne wanda muke gudanar dashi kowace shekara domin yiwa dabbobi allurar riga-kafin cutuka daban-daban, wanda a bara mun yi wa dabbobi kimanin miliyan daya da rabi, kuma a wannan shekara ma haka zamu yi. Sannan zamu kara da bai wa Fulaninmu tallafin dusa da sauran abincin dabbobi kyauta, domin rage musu wahalhalu.”

 

Bugu da kari, Sanata Lawan ya kaddamar da shirin bai wa al’ummar yankin sa tiyata kan matsaloli daban-daban kyauta, wanda ake gudanar dashi tun shekaru biyar da suka gabata, a asibitin kwararru na jihar Yobe dake Gashua, da Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) ta Nguru.

 

Ya ce tallafin ayyukan jinya kyauta domin masu fama da rashin lafiyar ido, tiyata kaba, duba lafiyar mata da yi wa wasu tiyata, gwajin cutar dadji, da sauran su, duk a kyauta ga kimanin mutum 5000.

 

Har wala yau, Sanata Lawan ya yi alkawarin gina Cibiyar kula da masu fama da cutar koda a Asibitin Kwararru ta Gashuwa domin saukake wa jama’ar yankin wahalhalun cutar. Kana da sake gyara hanyar Kwanar-Baderi zuwa Gir-gir, hanyar mota tare da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a sabuwar Sakandare Gwamnatin Tarayya dake Gashuwa, da sauran muhimman ayyuka a ziyarar da ya kai ta kwanaki uku a Yobe ta Arewa.

Lawan
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin ‘Yan Ta’adda Da Ke Kaduna

Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin 'Yan Ta'adda Da Ke Kaduna

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.