ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Nemi Gwamnati Ta Bunkasa Kiwon Dabbobi A Kasar Nan – Lawan

by Muhammad Maitela
4 years ago
Lawan

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, ya sha alwashin cewa zauren majalisar dattawan Nijeriya zai yi kokarin tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta tallafawa harkokin kiwon dabbobi a kasar nan- a matsayin sa na daya daga cikin manyan ginshikan ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Sanata Lawan ya sanar da hakan a karshen mako, a sa’ilin da yake kaddamar da allurar riga-kafi ga dabbobi kyauta a kauyen Jajuwa dake karamar hukumar Jakusko a jihar Yobe; shirin da Gidauniyar SAIL Foundation a karkashin sa ke daukar nauyin gudanar dashi tun shekarar 2018, domin al’ummar mazabar sa.

ADVERTISEMENT
  • Adalci Ne Kadai Zai Ce Ci Nijeriya, Inji Lawan Da Saraki Da Wike

Ya ce harkokin kiwo a Nijeriya ba kashin yasarwa bane, a matsayin sa na daya daga cikin manyan kadarkon da ke dauke da tattalin arzikin Nijeriya, “wanda kuma ya dace gwamnati ta tallafa wa harkar kiwo, saboda muke cin gajiyar fanni wajen ci gaban tattalin arzikinmu, sannan barin sa haka ba tare da agaza wa bangaren ba, to ba a yi masa adalci ba; duk sana’a ce mai zaman kanta, dole a tallafa wa sashen.”

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“A hannu guda kuma, suma bankuna harkar sana’a ce mai zaman kanta, wanda idan har gwamnati za ta tallafa wa masu tafiar dasu ba, ban ga dalilin da za a ki tallafa wa makiyaya dabbobi ba, wanda a zahiri ma sune suka fi kowa cancanta a tallafa musu, musamman gwamnatin tarayya.”

 

Sanata Lawan ya kara da cewa, “Zamu ci gaba da matsa wa Gwamnatin Tarayya lamba har sai ta tallafawa Fulani makiyaya dabbobi domin rage matsalolin da su ke fama da su lokaci zuwa lokaci.”

 

“Sannan a kokarinmu, a yau mun zo nan ne domin kaddamar da allurar rigakafin dabbobi, wadanda suka kunshi shanu, tumaki, da awakinmu, tare da sauran kananan dabbobi a wannan shiyya ta Yobe ta Arewa.”

 

“Wannan biki ne wanda muke gudanar dashi kowace shekara domin yiwa dabbobi allurar riga-kafin cutuka daban-daban, wanda a bara mun yi wa dabbobi kimanin miliyan daya da rabi, kuma a wannan shekara ma haka zamu yi. Sannan zamu kara da bai wa Fulaninmu tallafin dusa da sauran abincin dabbobi kyauta, domin rage musu wahalhalu.”

 

Bugu da kari, Sanata Lawan ya kaddamar da shirin bai wa al’ummar yankin sa tiyata kan matsaloli daban-daban kyauta, wanda ake gudanar dashi tun shekaru biyar da suka gabata, a asibitin kwararru na jihar Yobe dake Gashua, da Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) ta Nguru.

 

Ya ce tallafin ayyukan jinya kyauta domin masu fama da rashin lafiyar ido, tiyata kaba, duba lafiyar mata da yi wa wasu tiyata, gwajin cutar dadji, da sauran su, duk a kyauta ga kimanin mutum 5000.

 

Har wala yau, Sanata Lawan ya yi alkawarin gina Cibiyar kula da masu fama da cutar koda a Asibitin Kwararru ta Gashuwa domin saukake wa jama’ar yankin wahalhalun cutar. Kana da sake gyara hanyar Kwanar-Baderi zuwa Gir-gir, hanyar mota tare da wutar lantarki mai amfani da hasken rana a sabuwar Sakandare Gwamnatin Tarayya dake Gashuwa, da sauran muhimman ayyuka a ziyarar da ya kai ta kwanaki uku a Yobe ta Arewa.

Lawan
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin ‘Yan Ta’adda Da Ke Kaduna

Jiragen Sojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta A Sansanin 'Yan Ta'adda Da Ke Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.