Ɗaliban manyan makarantu a Nijeriya sun yi watsi da tsarin tallafin data da Gwamnatin Tarayya ta ke shiryawa, inda suka bukaci gwamnati ta samar da Wi-Fi kyauta a jami’o’i da sauran manyan makarantu.
Ɗaliban sun bayyana cewa samar da intanet kyauta a makarantu zai fi amfani wajen taimaka musu wajen bincike, karatu da samun kayan ilimi na zamani, maimakon tsarin bai wa ɗalibai tallafin data kadan-kadan.
Sun ce matsalar samun intanet mai araha na ci gaba da zama wani babban ƙalubale ga ɗalibai, musamman waɗanda ke dogaro da intanet wajen gudanar da ayyukan karatu da bincike.
A cewarsu, samar da Wi-Fi kyauta a harabar makarantu zai ba ɗalibai damar samun damar yin amfani da intanet ba tare da fuskantar ƙarin kuɗin data ba.
Ɗaliban sun kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta sake duba tsarin, tare da mayar da hankali kan samar da ingantaccen tsarin intanet na dindindin a cibiyoyin ilimi.














