ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

by Sadiq
35 minutes ago

Tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Alhaji Bamanga Muhammad Tukur, ya rasu yana da shekara 91.

Ɗaya daga cikin ’ya’yansa ne ya tabbatar wa maneman labarai rasuwarsa, inda ya ce ya rasu a gidansa da ke Abuja bayan lokaci da ya shafe yana fama da rashin lafiya.

Bamanga Tukur, wanda aka haife shi a Jihar Adamawa a shekarar 1935, ya kasance ɗan siyasa, ɗan kasuwa da kuma ma’aikacin gwamnati da ya riƙe muƙamai daban-daban a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya Taɓa Zama Gwamnan Gongola

Tukur ya zama Gwamnan tsohuwar Jihar Gongola a shekarar 1983.

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

Jihar Gongola ta haɗa yankunan da daga baya suka zama jihohin Adamawa da Taraba.

Sai dai bai daɗe yana mulki ba, domin sojoji sun karɓi mulki a watan Disamban 1983.

Kafin ya zama gwamna, Tukur ya riƙe babban muƙami a Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), inda ya yi aiki a matsayin babban manajan hukumar daga 1975 zuwa 1982.

Ya Taɓa Riƙe Ministan Masana’antu

Tukur ya koma aiki da Gwamnatin Tarayya a shekarun 1990, inda ya taɓa zama Ministan Masana’antu.

Baya ga harkokin siyasa, ya yi fice a fagen kasuwanci kuma ya riƙe muƙamai a ƙungiyoyin kasuwanci na Afirka, ciki har da African Business Roundtable da NEPAD Business Group.

Ya Shugabanci Jam’iyyar PDP

A watan Maris ɗin 2012, an zaɓi Tukur a matsayin Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa, wanda a lokacin ita ce jam’iyyar da ke mulkin Nijeriya.

Ya jagoranci jam’iyyar har zuwa watan Janairun 2014, lokacin da ya yi murabus a yayin da ake fama da rikice-rikice da rarrabuwar kai tsakanin manyan ’ya’yan jam’iyyar.

A lokacin shugabancinsa, wasu manyan ’ya’yan jam’iyyar PDP da gwamnoni sun samu saɓani da shugabancin jam’iyyar, lamarin da ya kai ga ƙirƙirar wani tsagi a jam’iyyar mai suna “New PDP”.

Rayuwar Bamanga Tukur cike ta ke da tarihi yin aiki a gwamnati, siyasa da kasuwanci, musamman a matakin tarayya da tsohuwar Jihar Gongola.

Shi ne kuma Tafidan Adamawa.

MASU ALAKA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro
Manyan Labarai

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 12, 2026
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

LABARAI MASU NASABA

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

September 12, 2026
Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

September 12, 2026
Gwamnatin Katsina

Abinda Kasafin Gwamna Raɗɗa Na Shekarar 2027 Ya Ƙunsa

September 12, 2026
Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

September 12, 2026
Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

September 12, 2026
Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.