Darakta Janar na Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu a zaɓen 2027, Sanata Abdul’aziz Abubakar Yari ya gana da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a wani taro a gidansa da ke Karamar Hukumar Talata Mafara.
Da yake magana da manema labarai jim kaɗan bayan taron, Sanata AA Yari ya ce ya yanke shawarar gana wa da masu ruwa da tsaki domin Neman cikakken goyon baya ga Shugaban Ƙasa a Zaben 2027. Ya tabbatar da cewa Jihar Zamfara za ta kada wa Shugaba Bola Ahmad Tinubu ƙuri’a mai yawa a lokacin zaɓe.
Ya ƙara da bayyana cewa dole ne ya fara aikinsa daga gida, domin yana sa ran samun cikakken goyon baya da ƙuri’u daga Zamfara, wadda jihar APC ce kuma shi ɗan Jihar ne. Haka kuma mutanen Zamfara suna yabawa Shugaban Ƙasa bisa wannan babban aiki na DG PCC.
Ya ce masu ruwa da tsaki sun ba da tabbacin cikakken goyon baya, da haɗin kai da ƙuri’u wajen tallafawa Shugaban Ƙasa ya sake dawowa mulki a 2027 na wa’adi na biyu.
Yari ya ce Shugaban Ƙasa yana yin iya ƙoƙarinsa wajen magance matsalar rashin tsaro, musamman a Zamfara da sauran sassan ƙasar. Ya ce PCC za ta yi yaƙin neman zaɓe ne bisa nasarorin da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya cimma waɗanda kowa ke iya gani.














